< Ƙidaya 5 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
OLELO mai la o Iehova ia Mose, i mai la,
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kori duk wanda yake da ciwon fatan jiki, ko mai ɗiga na kowane iri, ko wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin sansani.
E kauoha aku oe i na mamo a Iseraela, e hookuke aku i na lepero a pau iwaho o kahi hoomoana, a me na mea mai puha a pau, a me na mea a pau i haumia i ke kupapau.
3 Ka kori maza da mata ma; ka kai su bayan sansani domin kada su ƙazantar da sansani inda nake zama a cikinsu.”
O na kane a me na wahine ka oukou e hookuke aku ai iwaho o kahi hoomoana, i hoohaumia ole ai lakou i ko lakou mau wahi hoomoana, kahi a'u e noho nei iwaena konu.
4 Isra’ilawa suka yi haka; suka kore su daga sansanin. Suka aikata yadda dai Ubangiji ya umarci Musa.
Pela no i hana'i ka poe mamo a Iseraela, a hookuke aku la ia lakou iwaho o kahi hoomoana: me ka Iehova i olelo mai ai ia Mose, pela no na mamo a Iseraela i hana'i.
5 Ubangiji ya ce wa Musa,
Olelo mai la o Iehova ia Mose, i mai la,
6 “Gaya wa Isra’ilawa, ‘Sa’ad da namiji ko mace ya yi wa ɗan’uwansa laifi ta kowace hanya, ta yin haka, ya yi rashin aminci ga Ubangiji, mutumin kuwa ya yi laifi ke nan
E olelo aku oe i na mamo a Iseraela, Ina he kane paha he wahine paha, e hana i kekahi hewa, i ka mea a kanaka e hana'i, e lawehala ai ia Iehova, a i hewa ua kanaka la;
7 kuma dole yă furta zunubin da ya yi. Dole yă yi biya cikakkiyar diyya saboda laifinsa, yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar a kai, yă kuma bayar da shi duka ga wanda ya yi wa laifin.
Alaila, e hai mai lakou i ka hewa a lakou i hana'i: a e uku aku no ia i kana mea i lawehala ai, ma ke kumu o ia mea, a e hai pu me ia i ka hapalima hou aku o ia mea, a e haawi aku ia na ka mea ia ia kona lawehala ana.
8 Amma in mutumin da aka yi wa laifin ba shi da ɗan’uwa na kusa da za a biya diyya saboda laifin, sai diyyar tă zama ta Ubangiji, dole kuma a ba wa firist, haɗe da ragon da za a yi kafara da shi.
Ina paha aohe hoahanau no ua kanaka la, i ukuia'ku ai nona ka uku o ka hewa, alaila e ukuia'ku ka hewa ia Iehova, i ke kahuna hoi; he okoa ka hipakane kalahala, nana e kalaia'i ka hala nona.
9 Dukan tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka kawo wa firist za su zama nasa.
A o na mohai a pau no na mea laa a pau a ka poe mamo a Iseraeal, na mea a lakou e lawe mai ai i ke kahuna, e lilo ia nana.
10 Kowace tsarkakakkiyar kyauta da mutum ya kawo nasa ne, sai dai abin da ya ba wa firist, zai zama na firist.’”
Nana no hoi na mea laa a pau a kela kanaka keia kanaka: na mea a kekahi kanaka e haawi mai ai i ke kahuna, e lilo ia nana.
11 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Olelo mai la o Iehova ia Mose, i mai la,
12 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘In matar wani ta kauce, ta kuma yi rashin aminci gare shi
E olelo aku oe i na mamo a Iseraela, e i aku ia lakou, A i lalau ka wahine a kekahi kanaka, a e hana aku i ka mea e hewa ai ia ia,
13 ta wurin kwana da wani dabam, wannan kuwa ya kasance a ɓoye ga mijinta, rashin tsarkinta kuwa bai tonu ba (da yake babu shaida, ba a kuma kama ta tana yi ba),
A moe kolohe kekahi kanaka me ia, a ua hunaia ua mea la mai na maka aku o kana kane, a ua uhiia ia, a ua haumia oia; aohe mea hoike e ku e ia ia, aole hoi i loaa paka oia;
14 in kuma kishi ya sha kan mijinta kuma tana da ƙazanta, ko kuwa idan yana kishi yana kuma zatonta ko ma ba ta da ƙazanta
A i kau mai ka manao lili maluna o ke kane, a lili aku paha ia i kana wahine, a ua haumia kela: ina hoi e kau ka manao lili ia ia, a lili aku no ia i kana wahine, a ua haumia ole paha kela;
15 mijin zai kai matansa a gaban firist, yă kuma kawo hadayar abubuwan da ake bukata; abubuwa kamar, garin sha’ir garwa ɗaya, amma kada yă zuba mai a kan garin sha’ir, kada kuma yă sa turaren wuta a kansa, domin hadaya ce ta miji mai tuhumar matarsa da aka kawo domin gaskiya tă fito fili.
Alaila, e alakai aku ke kane i kana wahine i ke kahuna, a e lawe aku ia i kana mohai nona, i ka hapaumi o ka epa palaoa bale; aole ia e ninini i ka aila maluna, aole hoi e kau iho i ka libano maluna; no ka mea, he mohai ia no ka lili, he mohai hoomanao, e paipai ana e hoomanao i ka hewa.
16 “‘Firist zai kawo ta, yă sa tă tsaya a gaban Ubangiji.
A e alakai mai ke kahuna i ka wahine a kokoke, a e hoonoho ia ia imua o Iehova.
17 Sa’an nan zai ɗebi ruwa mai tsarki a tulun laka, yă zuba ƙurar da ya ɗebo daga daɓen tabanakul a cikin ruwan.
E lawe hoi ke kahuna i wahi wai laa iloko o ka ipu lepo; a e lawe ke kahuna i kekahi lepo o ka papalalo o ka halelewa, a e hahao iho iloko o ua wai la.
18 Bayan da firist ya sa matan ta tsaya a gaban Ubangiji, sai yă kunce gashin kanta, yă kuma sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi, yayinda shi kansa zai riƙe ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana.
A e hoonoho ke kahuna i ka wahine imua o Iehova, a e wehe i ka pale o ke poo o ua wahine la, a e waiho i ka mohai hoomanao iloko o kona lima, oia ka mohai no ka lili; a e paa ke kahuna i ka wai awaawa e hoopoino ai ma kona lima iho.
19 Sa’an nan firist zai sa tă yi rantsuwa, yă kuma ce mata, “In ba wani mutumin da ya kwana da ke kuma ba ki kauce kin ƙazantar da kanki yayinda kike auren mijinki ba, kada wannan ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, yă cuce ki.
A e kauoha aku ke kahuna ia ia ma ka hoohiki ana, a e elele aku ia i ka wahine, Ina i moe pu ole kekahi kanaka me oe, ina hoi i lalau ole ae oe i ka haumia me ka mea aole o kau kane iho, alaila ua kaawale oe i keia wai awaawa e hoopoino ai.
20 Amma in kin kauce yayinda kike auren mijinki, kika kuma ƙazantar da kanki ta wurin kwana da wani dabam da ba mijinki ba,”
Aka, ina he oiaio kou lalau ana'e i ka haumia me ka mea aole o kau kane iho, a ina i haumia io oe, a ua moe kekahi kanaka aole o kau kane me oe;
21 (a nan firist zai sa macen a ƙarƙashin la’anar rantsuwa cewa) “bari Ubangiji yă sa mutanenki su la’ance ki, su kuma yi Allah wadai da ke, sa’ad da Ubangiji ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbura.
Alaila, e kauoha aku ke kahuna i ka wahine ma ka olelo hoohiki no ka hoino ana; a e i aku ke kahuna i ua wahine ia, E hoolilo auanei o Iehova ia oe i mea poino, a i mea hoohikl ino ia iwaena o kou poe kanaka, i ka manawa a Iehova e hoowiwi iho ai i kou uha, a e hoopehu ai i kou opu:
22 Bari wannan ruwa mai jawo la’ana, yă shiga jikinki saboda cikinki yă kumbura, cinyarki kuma yă shanye.” “‘Sai macen tă ce, “Amin. Bari yă zama haka.”
A o keia wai hoopoino, e komo no ia iloko o kou opu i mea e pehu ai ka opu, a e wiwi ai ka uha. Alaila e olelo mai ka wahine, Amene, amene.
23 “‘Firist zai rubuta waɗannan la’anoni a littafi, sa’an nan yă wanke su cikin ruwa mai ɗaci.
A e palapala ke kahuna i keia mau hoino ana iloko o ka buke, a e holoi iho ia mea i ka wai awaawa.
24 Sai yă sa macen tă sha ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, wannan ruwa kuwa zai shiga cikinta yă kawo mata wahala mai zafi.
A e hooinu oia i ka wahine i ka wai awaawa, i ka mea e hoopoino ai: a o ka wai e hoopoino ai, e komo ia iloko ona, he mea awaawa.
25 Firist zai karɓi hadaya ta gari don kishi daga hannuwanta, yă kaɗa shi a gaban Ubangiji sa’an nan yă kawo a bagade.
Alaila e lawe ke kahuna i ka mohai no ka lili, mailoko mai o ka lima o ka wahine, a e hoali ae ia i ua mohai la imua o Iehova, a e kaumaha aku maluna o ke kuahu.
26 Sa’an nan firist zai ɗiba hatsi na hadaya cike da hannunsa don hadayar tunawa, yă kuma ƙone a bagade; bayan haka sai yă sa macen tă sha ruwan.
E lawe hoi ke kahuna i kauwahi o ka mohai a piha kona lima, i ka mea paipai manao, a e kuni ia i ke ahi maluna o ke kuahu; a mahope iho, e hooinu oia i ka wahine i ka wai.
27 In ta ƙazantar da kanta ta kuma ci amanar mijinta, to, yayinda aka sa tă sha ruwa mai jawo la’ana, ruwan zai shiga cikinta, yă jawo mata wahala mai zafi; cikinta zai kumbura, cinyarta kuma yă shanye, tă kuwa zama la’ananniya a cikin mutanenta.
A pau kona hooinu ana ia ia i ka wai, alaila, ina ua haumia ka wahine, a i hana oia i ka mea e hewa ai i kana kane, e komo no ua wai la ka mea e hoopoino ai iloko ona, he mea awaawa; a e pehu mai kona opu, a e wiwi iho kona uha; a e lilo ua wahine la i mea e hoinoia'i iwaena o kona hanauna kanaka.
28 Amma fa, in macen ba tă ƙazantar da kanta ba, ba tă kuma da ƙazanta, za a kuɓutar da ita daga laifin, za tă kuma iya haihuwa.
Ina hoi ua haumia ole ka wahine, he maemae no; alaila ua ola ia, a e hapai ia i na keiki.
29 “‘Wannan dai, ita ce dokar kishi sa’ad da mace ta kauce, ta kuma ƙazantar da kanta yayinda take aure da mijinta,
Oia ke kanawai no na lili ana, i ka manawa i huli ai ka wahine i ka mea aole o kana kane, a ua haumia oia;
30 ko kuma sa’ad da mijin yana kishi domin yana shakkar matarsa. Firist zai sa tă tsaya a gaban Ubangiji, yă kuma yi amfani da wannan doka gaba ɗaya a kanta.
A i ka manawa paha e kau ai ka manao lili maluna ona, a e lili aku ia i kana wahine, a e hoonoho aku ia ia imua o Iehova, a e hoopili aku ke kahuna i keia kanawai a pau ia ia:
31 Mijin zai zama marar laifi daga kowane laifi, amma matar za tă ɗauki muguntarta, idan ta yi laifin.’”
Alaila e kaawale ua kanaka la i ka hewa, a e lawe hoi ka wahine i kona hewa iho.

< Ƙidaya 5 >