< Ƙidaya 5 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh parla à Moïse, en disant:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kori duk wanda yake da ciwon fatan jiki, ko mai ɗiga na kowane iri, ko wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin sansani.
« Ordonne aux enfants d’Israël de faire sortir du camp quiconque à la lèpre et quiconque a une gonorrhée, et quiconque est souillé par un cadavre.
3 Ka kori maza da mata ma; ka kai su bayan sansani domin kada su ƙazantar da sansani inda nake zama a cikinsu.”
Hommes ou femmes, vous les ferez sortir du camp, afin qu’ils ne souillent pas leur camp, au milieu duquel j’habite. »
4 Isra’ilawa suka yi haka; suka kore su daga sansanin. Suka aikata yadda dai Ubangiji ya umarci Musa.
Les enfants d’Israël firent ainsi, et ils les firent sortir hors du camp; comme Yahweh l’avait ordonné à Moïse, ainsi firent les enfants d’Israël.
5 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh parla à Moïse, en disant:
6 “Gaya wa Isra’ilawa, ‘Sa’ad da namiji ko mace ya yi wa ɗan’uwansa laifi ta kowace hanya, ta yin haka, ya yi rashin aminci ga Ubangiji, mutumin kuwa ya yi laifi ke nan
« Dis aux enfants d’Israël: Si quelqu’un, homme ou femme, commet quelqu’un de tous les péchés qui cause un préjudice au prochain, en se rendant infidèle envers Yahweh, et qu’il se soit rendu coupable,
7 kuma dole yă furta zunubin da ya yi. Dole yă yi biya cikakkiyar diyya saboda laifinsa, yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar a kai, yă kuma bayar da shi duka ga wanda ya yi wa laifin.
il confessera son péché et il restituera en son entier l’objet mal acquis, en y ajoutant un cinquième; il le remettra à celui envers qui il s’est rendu coupable.
8 Amma in mutumin da aka yi wa laifin ba shi da ɗan’uwa na kusa da za a biya diyya saboda laifin, sai diyyar tă zama ta Ubangiji, dole kuma a ba wa firist, haɗe da ragon da za a yi kafara da shi.
Si celui-ci n’a pas de représentant à qui puisse être rendu l’objet du délit, cet objet revient à Yahweh, au prêtre, outre le bélier expiatoire avec lequel on fera l’expiation pour le coupable ».
9 Dukan tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka kawo wa firist za su zama nasa.
« Toute offrande prélevée sur les choses saintes que les enfants d’Israël présentent au prêtre, appartiendra à celui-ci;
10 Kowace tsarkakakkiyar kyauta da mutum ya kawo nasa ne, sai dai abin da ya ba wa firist, zai zama na firist.’”
les choses que tout homme aura consacré seront à lui; ce que chacun donne au prêtre lui appartiendra ».
11 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh parla à Moïse, en disant:
12 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘In matar wani ta kauce, ta kuma yi rashin aminci gare shi
« Parle aux enfants d’Israël, et dis-leur: Si une femme mariée se détourne et devient infidèle à son mari,
13 ta wurin kwana da wani dabam, wannan kuwa ya kasance a ɓoye ga mijinta, rashin tsarkinta kuwa bai tonu ba (da yake babu shaida, ba a kuma kama ta tana yi ba),
un autre homme ayant eu commerce avec elle, et que la chose soit cachée aux yeux de son mari, cette femme s’étant souillée en secret, sans qu’il y ait eu de témoin contre elle, et sans qu’elle ait été prise sur le fait:
14 in kuma kishi ya sha kan mijinta kuma tana da ƙazanta, ko kuwa idan yana kishi yana kuma zatonta ko ma ba ta da ƙazanta
— si le mari est saisi d’un esprit de jalousie et qu’il soit jaloux de sa femme qui s’est souillée, ou bien s’il est saisi d’un esprit de jalousie et qu’il soit jaloux de sa femme qui ne s’est pas souillée:
15 mijin zai kai matansa a gaban firist, yă kuma kawo hadayar abubuwan da ake bukata; abubuwa kamar, garin sha’ir garwa ɗaya, amma kada yă zuba mai a kan garin sha’ir, kada kuma yă sa turaren wuta a kansa, domin hadaya ce ta miji mai tuhumar matarsa da aka kawo domin gaskiya tă fito fili.
cet homme amènera sa femme au prêtre et il apportera une offrande à cause d’elle, un dixième d’épha de farine d’orge; il n’y versera pas d’huile et n’y mettra pas d’encens, car c’est une oblation de jalousie, une oblation de souvenir, qui rappelle une prévarication.
16 “‘Firist zai kawo ta, yă sa tă tsaya a gaban Ubangiji.
Le prêtre la fera approcher de l’autel et se tenir debout devant Yahweh.
17 Sa’an nan zai ɗebi ruwa mai tsarki a tulun laka, yă zuba ƙurar da ya ɗebo daga daɓen tabanakul a cikin ruwan.
Le prêtre prendra de l’eau sainte dans un vase de terre et, ayant pris de la poussière sur le sol de la Demeure, il la mettra dans l’eau.
18 Bayan da firist ya sa matan ta tsaya a gaban Ubangiji, sai yă kunce gashin kanta, yă kuma sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi, yayinda shi kansa zai riƙe ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana.
Le prêtre fera tenir la femme debout devant Yahweh, il dénouera la chevelure de la tête de la femme et lui posera sur les mains l’oblation de souvenir; c’est une oblation de jalousie. Le prêtre aura dans la main les eaux amères qui apportent la malédiction.
19 Sa’an nan firist zai sa tă yi rantsuwa, yă kuma ce mata, “In ba wani mutumin da ya kwana da ke kuma ba ki kauce kin ƙazantar da kanki yayinda kike auren mijinki ba, kada wannan ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, yă cuce ki.
Le prêtre adjurera la femme et lui dira: Si aucun homme n’a couché avec toi, et si tu ne t’es pas détournée pour te souiller, étant sous la puissance de ton mari, sois préservée de l’effet de ces eaux amères qui apportent la malédiction.
20 Amma in kin kauce yayinda kike auren mijinki, kika kuma ƙazantar da kanki ta wurin kwana da wani dabam da ba mijinki ba,”
Mais si, étant sous la puissance de ton mari, tu t’es détournée et t’es souillée, et si un autre homme que ton mari a couché avec toi:
21 (a nan firist zai sa macen a ƙarƙashin la’anar rantsuwa cewa) “bari Ubangiji yă sa mutanenki su la’ance ki, su kuma yi Allah wadai da ke, sa’ad da Ubangiji ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbura.
— le prêtre adjurera la femme par le serment d’imprécation, et lui dira: — Que Yahweh fasse de toi une malédiction et une exécration au milieu de ton peuple, en faisant maigrir tes flancs et enfler ton ventre,
22 Bari wannan ruwa mai jawo la’ana, yă shiga jikinki saboda cikinki yă kumbura, cinyarki kuma yă shanye.” “‘Sai macen tă ce, “Amin. Bari yă zama haka.”
et que ces eaux qui apportent la malédiction entrent dans tes entrailles pour te faire enfler le ventre et maigrir les flancs! Et la femme dira: Amen! Amen!
23 “‘Firist zai rubuta waɗannan la’anoni a littafi, sa’an nan yă wanke su cikin ruwa mai ɗaci.
Le prêtre écrira ces imprécations sur un rouleau, et il les effacera ensuite dans les eaux amères.
24 Sai yă sa macen tă sha ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, wannan ruwa kuwa zai shiga cikinta yă kawo mata wahala mai zafi.
Puis il fera boire à la femme les eaux amères qui apportent la malédiction, et les eaux qui apportent la malédiction entreront en elle pour lui être amères.
25 Firist zai karɓi hadaya ta gari don kishi daga hannuwanta, yă kaɗa shi a gaban Ubangiji sa’an nan yă kawo a bagade.
Le prêtre, ayant pris des mains de la femme l’oblation de jalousie, la balancera devant Yahweh, et l’approchera de l’autel;
26 Sa’an nan firist zai ɗiba hatsi na hadaya cike da hannunsa don hadayar tunawa, yă kuma ƙone a bagade; bayan haka sai yă sa macen tă sha ruwan.
il prendra une poignée de cette oblation comme mémorial, et il la fera fumer sur l’autel; et après cela, il fera boire les eaux à la femme.
27 In ta ƙazantar da kanta ta kuma ci amanar mijinta, to, yayinda aka sa tă sha ruwa mai jawo la’ana, ruwan zai shiga cikinta, yă jawo mata wahala mai zafi; cikinta zai kumbura, cinyarta kuma yă shanye, tă kuwa zama la’ananniya a cikin mutanenta.
Quand il lui fera boire les eaux, il arrivera, si elle s’est souillée et a été infidèle à son mari, que les eaux qui apportent la malédiction entreront en elle pour lui être amères: son ventre s’enflera, ses flancs maigriront, et cette femme sera une malédiction au milieu de son peuple.
28 Amma fa, in macen ba tă ƙazantar da kanta ba, ba tă kuma da ƙazanta, za a kuɓutar da ita daga laifin, za tă kuma iya haihuwa.
Mais si la femme ne s’est pas souillée et qu’elle soit pure, elle sera préservée, et elle aura des enfants.
29 “‘Wannan dai, ita ce dokar kishi sa’ad da mace ta kauce, ta kuma ƙazantar da kanta yayinda take aure da mijinta,
Telle est la loi sur la jalousie, quand une femme, étant sous la puissance de son mari, se détourne et se souille,
30 ko kuma sa’ad da mijin yana kishi domin yana shakkar matarsa. Firist zai sa tă tsaya a gaban Ubangiji, yă kuma yi amfani da wannan doka gaba ɗaya a kanta.
ou quand l’esprit de jalousie s’empare d’un mari et qu’il devient jaloux de sa femme: il fera tenir sa femme debout devant Yahweh, et le prêtre lui appliquera cette loi dans son entier.
31 Mijin zai zama marar laifi daga kowane laifi, amma matar za tă ɗauki muguntarta, idan ta yi laifin.’”
Le mari sera exempt de faute; mais la femme portera son iniquité ».

< Ƙidaya 5 >