< Ƙidaya 5 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
I mluvil Hospodin k Mojžíšovi, řka:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kori duk wanda yake da ciwon fatan jiki, ko mai ɗiga na kowane iri, ko wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin sansani.
Přikaž synům Izraelským, ať vyženou z stanů každého malomocného a každého trpícího tok semene, i každého nad mrtvým poškvrněného.
3 Ka kori maza da mata ma; ka kai su bayan sansani domin kada su ƙazantar da sansani inda nake zama a cikinsu.”
I muže i ženu vyženete, ven za stany vyženete je, aby nepoškvrňovali vojska těch, mezi nimiž já přebývám.
4 Isra’ilawa suka yi haka; suka kore su daga sansanin. Suka aikata yadda dai Ubangiji ya umarci Musa.
I učinili tak synové Izraelští, a vyhnali je ven za stany. Jakož byl mluvil Hospodin k Mojžíšovi, tak učinili synové Izraelští.
5 Ubangiji ya ce wa Musa,
Mluvil také Hospodin k Mojžíšovi, řka:
6 “Gaya wa Isra’ilawa, ‘Sa’ad da namiji ko mace ya yi wa ɗan’uwansa laifi ta kowace hanya, ta yin haka, ya yi rashin aminci ga Ubangiji, mutumin kuwa ya yi laifi ke nan
Mluv k synům Izraelským: Muž aneb žena, když učiní nějaký hřích lidský, dopouštěje se výstupku proti Hospodinu, a byla by vinna duše ta:
7 kuma dole yă furta zunubin da ya yi. Dole yă yi biya cikakkiyar diyya saboda laifinsa, yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar a kai, yă kuma bayar da shi duka ga wanda ya yi wa laifin.
Tedy vyzná hřích svůj, kterýž učinil, navrátí pak to, čímž vinen byl, v cele, a pátý díl přidá nad to, a dá tomu, proti komuž zavinil.
8 Amma in mutumin da aka yi wa laifin ba shi da ɗan’uwa na kusa da za a biya diyya saboda laifin, sai diyyar tă zama ta Ubangiji, dole kuma a ba wa firist, haɗe da ragon da za a yi kafara da shi.
A neměl-li by muž ten přítele, jemuž by nahradil tu škodu, pokuta dána buď Hospodinu a knězi, mimo skopce očištění, jímž očištěn býti má.
9 Dukan tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka kawo wa firist za su zama nasa.
Též všeliká obět všech věcí posvěcených od synů Izraelských, kterouž přinesou knězi, jemu se dostane.
10 Kowace tsarkakakkiyar kyauta da mutum ya kawo nasa ne, sai dai abin da ya ba wa firist, zai zama na firist.’”
Tak i věci posvěcené od kohokoli jemu se dostanou; a dal-li kdo co knězi, také jeho bude.
11 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Mluvil ještě Hospodin k Mojžíšovi, řka:
12 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘In matar wani ta kauce, ta kuma yi rashin aminci gare shi
Mluv k synům Izraelským a rci jim: Kdyby od některého muže uchýlila se žena, a dopustila by se výstupku proti němu,
13 ta wurin kwana da wani dabam, wannan kuwa ya kasance a ɓoye ga mijinta, rashin tsarkinta kuwa bai tonu ba (da yake babu shaida, ba a kuma kama ta tana yi ba),
Tak že by obýval někdo jiný s ní, a bylo by to skryto před očima muže jejího, a tajila by se, jsuci poškvrněna, a svědka by nebylo proti ní, a ona nebyla by postižena;
14 in kuma kishi ya sha kan mijinta kuma tana da ƙazanta, ko kuwa idan yana kishi yana kuma zatonta ko ma ba ta da ƙazanta
Pohnul-li by se duch muže horlivostí velikou, tak že by horlil proti ženě své, kteráž by poškvrněna byla; aneb pohnul-li by se duch muže velikou horlivostí, tak že by horlil proti ženě své, kteráž by poškvrněna nebyla:
15 mijin zai kai matansa a gaban firist, yă kuma kawo hadayar abubuwan da ake bukata; abubuwa kamar, garin sha’ir garwa ɗaya, amma kada yă zuba mai a kan garin sha’ir, kada kuma yă sa turaren wuta a kansa, domin hadaya ce ta miji mai tuhumar matarsa da aka kawo domin gaskiya tă fito fili.
Tedy přivede muž ženu svou k knězi, a přinese obět její při ní, desátý díl efi mouky ječné. Nenalejeť na ni oleje, aniž dá na ni kadidla; nebo obět veliké horlivosti jest, obět suchá pamětná, uvozující v pamět nepravost.
16 “‘Firist zai kawo ta, yă sa tă tsaya a gaban Ubangiji.
I bude ji kněz obětovati, a postaví ji před Hospodinem.
17 Sa’an nan zai ɗebi ruwa mai tsarki a tulun laka, yă zuba ƙurar da ya ɗebo daga daɓen tabanakul a cikin ruwan.
A nabere vody svaté do nádoby hliněné, a vezma prachu, kterýž jest na zemi v příbytku, dá jej do té vody.
18 Bayan da firist ya sa matan ta tsaya a gaban Ubangiji, sai yă kunce gashin kanta, yă kuma sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi, yayinda shi kansa zai riƙe ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana.
Potom postaví kněz ženu tu před Hospodinem, a odkryje hlavu její, a dá jí do rukou obět suchou pamětnou, kteráž jest obět veliké horlivosti; v ruce pak kněze bude voda hořká zlořečená.
19 Sa’an nan firist zai sa tă yi rantsuwa, yă kuma ce mata, “In ba wani mutumin da ya kwana da ke kuma ba ki kauce kin ƙazantar da kanki yayinda kike auren mijinki ba, kada wannan ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, yă cuce ki.
I zaklínati bude ji kněz a řekne k ní: Jestliže neobcoval s tebou žádný, a jestliže jsi neuchýlila se k nečistotě od muže svého, budiž čistá od vody této hořké zlořečené.
20 Amma in kin kauce yayinda kike auren mijinki, kika kuma ƙazantar da kanki ta wurin kwana da wani dabam da ba mijinki ba,”
Paklis se uchýlila od muže svého a nečistá jsi, a obcoval-li někdo jiný s tebou kromě manžela tvého,
21 (a nan firist zai sa macen a ƙarƙashin la’anar rantsuwa cewa) “bari Ubangiji yă sa mutanenki su la’ance ki, su kuma yi Allah wadai da ke, sa’ad da Ubangiji ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbura.
(Zaklínati pak bude kněz tu ženu, čině klatbu zlořečenství, a řekne jí: ) Dejž tebe Hospodin v zlořečení a v prokletí u prostřed lidu tvého, dopustě, aby lůno tvé hnilo a břicho tvé oteklo.
22 Bari wannan ruwa mai jawo la’ana, yă shiga jikinki saboda cikinki yă kumbura, cinyarki kuma yă shanye.” “‘Sai macen tă ce, “Amin. Bari yă zama haka.”
Vejdiž voda zlořečená tato do života tvého, aby oteklo břicho tvé, a lůno tvé shnilo. I odpoví žena ta: Amen, amen.
23 “‘Firist zai rubuta waɗannan la’anoni a littafi, sa’an nan yă wanke su cikin ruwa mai ɗaci.
Napíše pak všecko zlořečenství toto do knihy, a smyje je tou vodou hořkou.
24 Sai yă sa macen tă sha ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, wannan ruwa kuwa zai shiga cikinta yă kawo mata wahala mai zafi.
I dá ženě, aby pila vodu hořkou a zlořečenou; a vejdeť do ní voda zlořečená, a obrátí se v hořkosti.
25 Firist zai karɓi hadaya ta gari don kishi daga hannuwanta, yă kaɗa shi a gaban Ubangiji sa’an nan yă kawo a bagade.
Potom vezme kněz z ruky ženy obět veliké horlivosti, a obraceti ji bude sem i tam před Hospodinem, a bude ji obětovati na oltáři.
26 Sa’an nan firist zai ɗiba hatsi na hadaya cike da hannunsa don hadayar tunawa, yă kuma ƙone a bagade; bayan haka sai yă sa macen tă sha ruwan.
A vezma plnou hrst pamětného jejího z oběti suché, páliti to bude na oltáři; a potom dá vypíti ženě tu vodu.
27 In ta ƙazantar da kanta ta kuma ci amanar mijinta, to, yayinda aka sa tă sha ruwa mai jawo la’ana, ruwan zai shiga cikinta, yă jawo mata wahala mai zafi; cikinta zai kumbura, cinyarta kuma yă shanye, tă kuwa zama la’ananniya a cikin mutanenta.
A když jí dá píti tu vodu, stane se, jestliže nečistá byla, a dopustila se výstupku proti muži svému, že vejde do ní voda zlořečená, a obrátí se v hořkost, i odme se břicho její, a vyhnije lůno její; i bude žena ta v zlořečení u prostřed lidu svého.
28 Amma fa, in macen ba tă ƙazantar da kanta ba, ba tă kuma da ƙazanta, za a kuɓutar da ita daga laifin, za tă kuma iya haihuwa.
Pakli není poškvrněna žena ta, ale čistá jest, tedy bez viny bude, a roditi bude děti.
29 “‘Wannan dai, ita ce dokar kishi sa’ad da mace ta kauce, ta kuma ƙazantar da kanta yayinda take aure da mijinta,
Ten jest zákon veliké horlivosti, když by se uchýlila žena od muže svého, a byla by poškvrněna,
30 ko kuma sa’ad da mijin yana kishi domin yana shakkar matarsa. Firist zai sa tă tsaya a gaban Ubangiji, yă kuma yi amfani da wannan doka gaba ɗaya a kanta.
Aneb když by se pohnul duch veliké horlivosti v manželu, tak že by horlil velmi proti ženě své, aby postavil ji před Hospodinem, a aby vykonal při ní kněz všecko vedlé zákona tohoto.
31 Mijin zai zama marar laifi daga kowane laifi, amma matar za tă ɗauki muguntarta, idan ta yi laifin.’”
I bude ten muž očištěn od hříchu, žena pak ponese nepravost svou.