< Ƙidaya 5 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Jahve reče Mojsiju:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kori duk wanda yake da ciwon fatan jiki, ko mai ɗiga na kowane iri, ko wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin sansani.
“Naredi Izraelcima da iz tabora odstrane svakoga gubavca, svakoga koji imadne izljev i svakoga koji se onečisti mrtvim tijelom.
3 Ka kori maza da mata ma; ka kai su bayan sansani domin kada su ƙazantar da sansani inda nake zama a cikinsu.”
Odstranite i muške i ženske! Izvan tabora ih istjerajte da ne onečiste svoje tabore u kojima ja boravim među njima.”
4 Isra’ilawa suka yi haka; suka kore su daga sansanin. Suka aikata yadda dai Ubangiji ya umarci Musa.
Izraelci tako učine: istjeraju ih iz tabora. Kako je Jahve rekao Mojsiju, tako Izraelci učine.
5 Ubangiji ya ce wa Musa,
Jahve reče Mojsiju:
6 “Gaya wa Isra’ilawa, ‘Sa’ad da namiji ko mace ya yi wa ɗan’uwansa laifi ta kowace hanya, ta yin haka, ya yi rashin aminci ga Ubangiji, mutumin kuwa ya yi laifi ke nan
“Kaži Izraelcima: Kad koji čovjek ili žena počini bilo kakav grijeh na štetu čovjeka ogriješivši se protiv Jahve, i osjeti se krivim,
7 kuma dole yă furta zunubin da ya yi. Dole yă yi biya cikakkiyar diyya saboda laifinsa, yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar a kai, yă kuma bayar da shi duka ga wanda ya yi wa laifin.
neka prizna počinjeni grijeh, nadoknadi štetu što bolje može te još doda tome petinu i dadne onome kome je nanio nepravdu.
8 Amma in mutumin da aka yi wa laifin ba shi da ɗan’uwa na kusa da za a biya diyya saboda laifin, sai diyyar tă zama ta Ubangiji, dole kuma a ba wa firist, haɗe da ragon da za a yi kafara da shi.
Ako čovjek ne bi imao bližeg rođaka kome bi se nadoknada mogla uručiti, dužna nadoknada pripada Jahvi za svećenika, ne računajući u to pomirbenoga ovna kojim će svećenik izvršiti nad krivcem obred pomirenja.
9 Dukan tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka kawo wa firist za su zama nasa.
I svaka podizanica od svih posvećenih stvari što ih Izraelci svećeniku donose njemu pripada.
10 Kowace tsarkakakkiyar kyauta da mutum ya kawo nasa ne, sai dai abin da ya ba wa firist, zai zama na firist.’”
Svakome idu stvari koje je posvetio; i neka svećeniku bude ono što njemu tko dadne.”
11 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Jahve reče Mojsiju:
12 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘In matar wani ta kauce, ta kuma yi rashin aminci gare shi
“Govori Izraelcima i reci im: Ako nekome žena pođe stranputicom te mu se iznevjeri
13 ta wurin kwana da wani dabam, wannan kuwa ya kasance a ɓoye ga mijinta, rashin tsarkinta kuwa bai tonu ba (da yake babu shaida, ba a kuma kama ta tana yi ba),
i netko s njom legne, ali to ostane sakriveno očima njezina muža i žena ostane neotkrivena iako se oskvrnula te protiv nje ne bude svjedoka budući da u činu nije bila uhvaćena -
14 in kuma kishi ya sha kan mijinta kuma tana da ƙazanta, ko kuwa idan yana kishi yana kuma zatonta ko ma ba ta da ƙazanta
i sad muža obuzme duh ljubomore i on postane ljubomoran na svoju ženu koja se oskvrnula; ili ako ga spopadne duh ljubomore te postane ljubomoran na svoju ženu a da se ona nije oskvrnula -
15 mijin zai kai matansa a gaban firist, yă kuma kawo hadayar abubuwan da ake bukata; abubuwa kamar, garin sha’ir garwa ɗaya, amma kada yă zuba mai a kan garin sha’ir, kada kuma yă sa turaren wuta a kansa, domin hadaya ce ta miji mai tuhumar matarsa da aka kawo domin gaskiya tă fito fili.
neka taj muž dovede svoju ženu svećeniku. Neka za nju donese prinos: desetinu efe ječmenog brašna. Neka po njemu ne polijeva ulja niti na nj stavlja tamjana, jer to je prinosnica za ljubomoru, spomen-prinosnica da podsjeti na grijeh.
16 “‘Firist zai kawo ta, yă sa tă tsaya a gaban Ubangiji.
Neka svećenik povede tu ženu i postavi je pred Jahvu.
17 Sa’an nan zai ɗebi ruwa mai tsarki a tulun laka, yă zuba ƙurar da ya ɗebo daga daɓen tabanakul a cikin ruwan.
Sad neka svećenik uzme posvećene vode u kakvu zemljanu posudu i, uzevši prašine što je na podu Prebivališta, neka je svećenik ubaci u vodu.
18 Bayan da firist ya sa matan ta tsaya a gaban Ubangiji, sai yă kunce gashin kanta, yă kuma sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi, yayinda shi kansa zai riƙe ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana.
Pošto je svećenik postavio ženu pred Jahvu, neka joj otkrije glavu a na njezine ruke stavi spomen-prinosnicu, to jest žitnu prinosnicu za ljubomoru, s svećenik neka drži u ruci vodu gorčine i prokletstva.
19 Sa’an nan firist zai sa tă yi rantsuwa, yă kuma ce mata, “In ba wani mutumin da ya kwana da ke kuma ba ki kauce kin ƙazantar da kanki yayinda kike auren mijinki ba, kada wannan ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, yă cuce ki.
Zatim neka svećenik ženu zakune. Neka joj reče: 'Ako nikad čovjek s tobom nije ležao te ako nisi išla stranputicom i oskvrnula se dok si bila pod vlašću svoga muža, budi pošteđena od ove vode gorčine i prokletstva!
20 Amma in kin kauce yayinda kike auren mijinki, kika kuma ƙazantar da kanki ta wurin kwana da wani dabam da ba mijinki ba,”
Ali ako si išla stranputicom dok si bila pod vlašću svoga muža te se oskvrnula; ako je koji čovjek osim tvoga muža legao s tobom ...'
21 (a nan firist zai sa macen a ƙarƙashin la’anar rantsuwa cewa) “bari Ubangiji yă sa mutanenki su la’ance ki, su kuma yi Allah wadai da ke, sa’ad da Ubangiji ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbura.
Ovdje neka svećenik zakune ženu ovom kletvom: neka joj rekne: Jahve te postavio za prokletstvo i kletvu među tvojim narodom, učinio da ti uvene rodnica i da ti se utroba nadme!
22 Bari wannan ruwa mai jawo la’ana, yă shiga jikinki saboda cikinki yă kumbura, cinyarki kuma yă shanye.” “‘Sai macen tă ce, “Amin. Bari yă zama haka.”
Neka ova voda prokletstva zađe u tvoju utrobu! Trbuh ti se od nje naduo, a rodnica uvenula! - A žena neka poprati: Amen! Amen!
23 “‘Firist zai rubuta waɗannan la’anoni a littafi, sa’an nan yă wanke su cikin ruwa mai ɗaci.
Potom neka ta prokletstva svećenik napiše na list pa ih ispere u vodu gorčine.
24 Sai yă sa macen tă sha ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, wannan ruwa kuwa zai shiga cikinta yă kawo mata wahala mai zafi.
Onda neka ženu napoji vodom gorčine i prokletstva, da bi se voda gorčine po njoj razišla i napunila je gorkošću.
25 Firist zai karɓi hadaya ta gari don kishi daga hannuwanta, yă kaɗa shi a gaban Ubangiji sa’an nan yă kawo a bagade.
Neka svećenik onda uzme iz ženine ruke prinosnicu za ljubomoru, prinese je pred Jahvom kao žrtvu prikaznicu te je donese na žrtvenik.
26 Sa’an nan firist zai ɗiba hatsi na hadaya cike da hannunsa don hadayar tunawa, yă kuma ƙone a bagade; bayan haka sai yă sa macen tă sha ruwan.
Zagrabivši od prinosnice punu pregršt kao spomen-žrtvu, neka to sažeže u kad na žrtveniku. Napokon, neka ženu napoji vodom.
27 In ta ƙazantar da kanta ta kuma ci amanar mijinta, to, yayinda aka sa tă sha ruwa mai jawo la’ana, ruwan zai shiga cikinta, yă jawo mata wahala mai zafi; cikinta zai kumbura, cinyarta kuma yă shanye, tă kuwa zama la’ananniya a cikin mutanenta.
Pošto je napoji vodom, bude li oskvrnuta iznevjerivši se svome mužu, voda prokletstva ući će u nju i napunit će je gorčinom; njezina će se utroba naduti a rodnica uvenuti - ta će žena postati prokletstvom u svome narodu.
28 Amma fa, in macen ba tă ƙazantar da kanta ba, ba tă kuma da ƙazanta, za a kuɓutar da ita daga laifin, za tă kuma iya haihuwa.
A ako žena ne bude oskvrnuta nego nevina, neće joj biti ništa i imat će djece.
29 “‘Wannan dai, ita ce dokar kishi sa’ad da mace ta kauce, ta kuma ƙazantar da kanta yayinda take aure da mijinta,
To je obred u slučaju ljubomore, kad žena pođe stranputicom i oskvrne se dok je pod vlašću svoga muža;
30 ko kuma sa’ad da mijin yana kishi domin yana shakkar matarsa. Firist zai sa tă tsaya a gaban Ubangiji, yă kuma yi amfani da wannan doka gaba ɗaya a kanta.
ili kad kojega čovjeka obuzme duh ljubomore te postane ljubomoran na svoju ženu. Neka, dakle, postavi svoju ženu pred Jahvu, a svećenik neka nad njom izvrši sav ovaj obred.
31 Mijin zai zama marar laifi daga kowane laifi, amma matar za tă ɗauki muguntarta, idan ta yi laifin.’”
Neka je muž slobodan od krivnje, a žena neka snosi svoju krivnju.”