< Ƙidaya 4 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying,
2 “Ku yi ƙidaya Kohatawa daga Lawiyawa, bisa ga kabilarsu da iyalansu.
Take the sum of the children of Caath from the midst of the sons of Levi, after their families, according to the houses of their fathers' households;
3 Ku ƙidaya dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin da suka zo domin aiki a Tentin Sujada.
from twenty-five years old and upward until fifty years, every one that goes in to minister, to do all the works in the tabernacle of witness.
4 “Ga aikin Kohatawa a Tentin Sujada, kulawa da kayayyaki mafi tsarki.
And these are the works of the sons of Caath in the tabernacle of witness; it is most holy.
5 Lokacin da za a tashi daga sansani, Haruna da’ya’yansa za su shiga ciki su kunce labulen kāriya, su rufe Akwatin Alkawari da shi.
And Aaron and his sons shall go in, when the camp is about to move, and shall take down the shadowing veil, and shall cover with it the ark of the testimony.
6 Sa’an nan su rufe shi da fatun shanun teku, su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi a bisansa, su sa masa sandunansa.
And they shall put on it a cover, even a blue skin, and put on it above a garment all of blue, and shall put the staves through [the rings].
7 “A bisa teburin Burodin Ajiyewa, za su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi, a kansa kuma su sa farantai, kwanoni da manyan kwanoni, da tuluna don hadayun sha; da burodin da zai ci gaba da kasancewa a kansa.
And they shall put on the table set forth for show-bread a cloth all of purple, and the dishes, and the censers, and the cups, and the vessels with which one offers drink-offerings; and the continual loaves shall be upon it.
8 A bisa waɗannan za su shimfiɗa jan zane, su rufe su da fatun shanun teku, su kuma zura masa sandunansa.
And they shall put upon it a scarlet cloth, and they shall cover it with a blue covering of skin, and they shall put the staves into it.
9 “Za su ɗauki zane mai ruwan shuɗi su rufe wurin ajiye fitilan da yake don fitilu, tare da fitilunsa, lagwaninsa da farantansa, da dukan tulunansa don man amfaninsu.
And they shall take a blue covering, and cover the candlestick that gives light, and its lamps, and its snuffers, and its funnels, and all the vessels of oil with which they minister.
10 Sa’an nan su naɗe shi da kuma dukan kayayyakinsa a cikin fatar shanun teku, su sa shi a kan sandan ɗaukarsa.
And they shall put it, and all its vessels, into a blue skin cover; and they shall put it on bearers.
11 “A kan bagaden zinariya, za su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi, su kuma rufe shi da fatar shanun teku, sai a zura masa sandunansa.
And they shall put a blue cloth for a cover on the golden altar, and shall cover it with a blue skin cover, and put in its staves.
12 “Za su ɗauki dukan kayayyakin da ake amfani da su a wuri mai tsarki, su nannaɗe su da zane mai ruwan shuɗi, su rufe shi da fatar shanun teku, sa’an nan a sa su a kan sandan ɗaukarsa.
And they shall take all the instruments of service, with which they minister in the sanctuary: and shall place them in a cloth of blue, and shall cover them with blue skin covering, and put them upon staves.
13 “Za su kwashe tokar da take a bagaden tagulla, su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi a bisansa.
And he shall put the covering on the altar, and they shall cover it with a cloth all of purple.
14 Sa’an nan su sa a kansa dukan kayayyakin da aka yi amfani da su a bagaden, haɗe da farantai don wuta, cokula masu yatsu don nama, manyan cokula, da darunan yayyafawa. A kansa za su shimfiɗa murfi na fatun shanun teku, su zura sandunan ɗaukarsa.
And they shall put upon it all the vessels with which they minister upon it, and the fire-pans, and the flesh hooks, and the cups, and the cover, and all the vessels of the altar; and they shall put on it a blue cover of skins, and shall put in its staves; and they shall take a purple cloth, and cover the laver and its foot, and they shall put it into a blue cover of skin, and put it on bars.
15 “Bayan Haruna da’ya’yansa suka gama rufe kayayyaki masu tsarki da dukan abubuwa masu tsarki, sa’ad da kuma aka shirya tashi daga sansani, sai Kohatawa su zo gaba, su ɗauka. Amma kada su taɓa abubuwa masu tsarki, don kada su mutu. Kohatawa za su ɗauki abubuwan da suke cikin Tentin Sujada.
And Aaron and his sons shall finish covering the holy things, and all the holy vessels, when the camp begins to move; and afterwards the sons of Caath shall go in to take up [the furniture]; but shall not touch the holy things, lest they die: these shall the sons of Caath bear in the tabernacle of witness.
16 “Eleyazar ɗan Haruna firist zai lura da man fitila da turare da hadaya ta gari na kullum da kuma keɓaɓɓen mai. Shi ne zai lura da dukan tabanakul da duk abin da yake cikinsa da kuma kayayyaki da abubuwan masu tsarki.”
Eleazar the son of Aaron the priest is overseer—the oil of the light, and the incense of composition, and the daily meat-offering and the anointing oil, are his charge; even the oversight of the whole tabernacle, and all things that are in it in the holy place, in all the works.
17 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying,
18 “Ku tabbata cewa ba a kawar da zuriyar Kohatawa daga Lawiyawa ba.
You shall not destroy the family of Caath from the tribe out of the midst of the Levites.
19 Saboda su rayu, kada su mutu sa’ad da suka zo kusa da abubuwa mafi tsarki, a yi musu wannan, wato, Haruna da’ya’yansa za su shiga wuri mai tsarki su ba wa kowane mutum aikinsa da kuma abin da zai ɗauka.
This do you to them, and they shall live and not die, when they approach the holy of holies: Let Aaron and his sons advance, and they shall place them each in his post for bearing.
20 Amma kada Kohatawa su shiga don su dubi abubuwa masu tsarki, ko na ɗan ƙanƙanin lokaci, in ba haka ba za su mutu.”
And [so] they shall by no means go in to look suddenly upon the holy things, and die.
21 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying,
22 “Ka ƙidaya mutanen Gershon bisa ga iyalansu da kabilarsu.
Take the sum of the children of Gedson, and these according to the houses of their lineage, according to their families.
23 Ka ƙidaya maza masu shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada.
Take the number of them from five and twenty years old and upwards until the age of fifty, every one that goes in to minister, to do his business in the tabernacle of witness.
24 “Ga aikin kabilar Gershonawa yayinda suke aiki, suke kuma ɗaukar kaya.
This [is] the public service of the family of Gedson, to minister and to bear.
25 Za su ɗauki labulen tabanakul, Tentin Sujada, kayan da za a rufe shi, da kuma kayan da za a rufe shi daga waje na fatun rufuwa na shanun teku, labulen ƙofar Tentin Sujada,
And they shall bear the skins of the tabernacle, and the tabernacle of witness, and its veil, and the blue cover that was on it above, and the cover of the door of the tabernacle of witness.
26 labulen filin da yake kewaye da tabanakul da bagade, labulen ƙofa, igiyoyi da kuma dukan abubuwan da ake amfani da su wajen hidima. Geshonawa za su yi dukan abin da ya kamata a yi da waɗannan abubuwa.
And all the curtains of the court which were upon the tabernacle of witness, and the appendages, and all the vessels of service that they minister with they shall attend to.
27 Dukan hidimominsu, ko na ɗauko, ko kuma na yin wani aiki, za a yi su ne bisa ga umarnin Haruna da’ya’yansa. Za ka ba su dukan kayan da za su ɗauka a matsayin hakkinsu.
According to the direction of Aaron and his sons shall be the ministry of the sons of Gedson, in all their ministries, and in all their works; and you shall take account of them by name in all things borne by them.
28 Wannan shi ne hidimar da kabilar Gershonawa za su yi a Tentin Sujada. Ayyukansu za su kasance bisa ga umarnin Itamar ɗan Haruna firist.
This is the service of the sons of Gedson in the tabernacle of witness, and their charge by the hand of Ithamar the son of Aaron the priest.
29 “Ka ƙidaya kabilar Merari bisa ga kabilarsu da iyalansu.
The sons of Merari according to their families, according to the houses of their lineage, take you the number of them.
30 Ka ƙidaya maza daga masu shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada.
Take the number of them from five and twenty years old and upwards until fifty years old, every one that goes in to perform the services of the tabernacle of witness.
31 Ga aikinsu sa’ad da suke hidima a Tentin Sujada, za su ɗauki katakan tabanakul, sandunansa da dogayen sandunansa, da rammukansa,
And these are the charges of the things borne by them according to all their works in the tabernacle of witness: they shall bear the chapiters of the tabernacle, and the bars, and its pillars, and its sockets, and the veil, and [there shall be] their sockets, and their pillars, and the curtain of the door of the tabernacle.
32 har ma da dogayen sandunan kewayen filin da rammukansu, turakun tenti, igiyoyi, da dukan kayayyaki, da kuma dukan abubuwan da suke dangane da amfaninsu. Ka ba wa kowane mutum ayyuka na musamman da zai yi.
And they shall bear the pillars of the court round about, and [there shall be] their sockets, and [they shall bear] the pillars of the veil of the door of the court, and their sockets and their pins, and their cords, and all their furniture, and all their instruments of service: take you their number by name, and all the articles of the charge of the things borne by them.
33 Wannan ce hidimar da mutanen Merari za su yi a aikin Tentin Sujada, a ƙarƙashin jagorancin Itamar ɗan Haruna, firist.”
This is the ministration of the family of the sons of Merari in all their works in the tabernacle of witness, by the hand of Ithamar the son of Aaron the priest.
34 Musa, Haruna da kuma shugabannin jama’a, suka ƙidaya Kohatawa ta kabilarsu da kuma iyalansu.
And Moses and Aaron and the rulers of Israel took the number of the sons of Caath according to their families, according to the houses of their lineage;
35 Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada,
from five and twenty years old and upwards to the age of fifty years, every one that goes in to minister and do service in the tabernacle of witness.
36 da aka ƙidaya, kabila-kabila, su 2,750 ne.
And the numbering of them according to their families was two thousand, seven hundred and fifty.
37 Jimillar dukan waɗanda suke na kabilan Kohatawa, waɗanda suka yi hidimar aiki a Tentin Sujada ke nan. Musa da Haruna sun ƙidaya su bisa ga umarnin Ubangiji.
This is the numbering of the family of Caath, every one that ministers in the tabernacle of witness, as Moses and Aaron numbered them by the word of the Lord, by the hand of Moses.
38 Aka ƙidaya mazan Gershonawa ta kabilansu da kuma iyalansu.
And the sons of Gedson were numbered according to their families, according to the houses of their lineage,
39 Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada,
from five and twenty years old and upward till fifty years old, every one that goes in to minister and to do the services in the tabernacle of witness.
40 da aka ƙidaya kabila-kabila da kuma iyali-iyali, su 2,630 ne.
And the numbering of them according to their families, according to the houses of their lineage, [was] two thousand six hundred and thirty.
41 Jimillar waɗanda suke na kabilar Gershonawa ke nan, waɗanda suka yi hidimar aiki a Tentin Sujada. Musa da Haruna sun ƙidaya su bisa ga umarnin Ubangiji.
This [is] the numbering of the family of the sons of Gedson, every one who ministers in the tabernacle of witness; whom Moses and Aaron numbered by the word of the Lord, by the hand of Moses.
42 Aka ƙidaya mazan Merari ta kabilarsu da kuma iyalansu.
And also the family of the sons of Merari were numbered according to their divisions, according to the house of their fathers;
43 Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada,
from five and twenty years old and upward till fifty years old, every one that goes in to minister in the services of the tabernacle of witness.
44 da aka ƙidaya kabila-kabila, su 3,200 ne.
And the numbering of them according to their families, according to the houses of their lineage, [was] three thousand and two hundred.
45 Jimillar waɗanda suke na kabilar Merari ke nan. Musa da Haruna suka ƙidaya su bisa ga umarnin Ubangiji.
This [is] the numbering of the family of the sons of Merari, whom Moses and Aaron numbered by the word of the Lord, by the hand of Moses.
46 Saboda haka, Musa, Haruna da shugabannin Isra’ila, suka ƙidaya dukan Lawiyawa kabila-kabila da kuma iyali-iyali.
All that were numbered, whom Moses and Aaron and the rulers of Israel numbered, [namely], the Levites, according to their families and according to the houses of their lineage,
47 Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki da kuma ɗaukar Tentin Sujada
from five and twenty years old and upward till fifty years old, every one that goes in to the service of the works, and the [charge of] the things that are carried in the tabernacle of witness.
48 jimillarsu ta kai 8,580.
And they that were numbered were eight thousand five hundred and eighty.
49 Bisa ga umarnin Ubangiji ta wurin Musa, aka ba kowa aikinsa, aka kuma faɗa musu abin da za su ɗauka. Ta haka aka ƙidaya su, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
He reviewed them by the word of the Lord by the hand of Moses, appointing each man severally over their [respective] work, and over their burdens; and they were numbered, as the Lord commanded Moses.

< Ƙidaya 4 >