< Ƙidaya 36 >

1 Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
Los jefes de las casas paternas de la familia de Galaad, descendiente de Maquir, hijo de Manasés, de las familias de los hijos de José, se presentaron ante Moisés y ante los jefes de las casas paternas de los hijos de Israel
2 Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
y dijeron: Yavé te ordenó a ti, nuestro ʼadón, que reparta la tierra por suerte a los hijos de Israel. También a ti, nuestro ʼadón, le fue ordenado por Yavé que diera la herencia de nuestro hermano Zelofejad a sus hijas.
3 To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
Pero si ellas se casan con uno de otra tribu israelita, su heredad sería sustraída de la herencia de nuestros antepasados. Así que la heredad de la tribu a la cual ellas pasen aumentará, y la que nos tocó a nosotros disminuirá.
4 Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
Cuando llegue el jubileo para los hijos de Israel, su herencia sería añadida a la heredad de la tribu de sus esposos, y así su herencia se sustraerá de la heredad de la tribu de nuestros antepasados.
5 Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
Entonces Moisés ordenó a los hijos de Israel, por mandato de Yavé: Dicen bien los de la tribu de los hijos de José.
6 Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
Esto es lo que Yavé ordenó con respecto a las hijas de Zelofejad: Cásense con quien ellas quieran, con tal que se casen dentro de la familia de la tribu de su padre,
7 Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
para que la herencia de los hijos de Israel no sea traspasada de tribu en tribu, sino que cada uno de los hijos de Israel conserve la herencia de la tribu de sus antepasados.
8 Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
También toda hija que tenga herencia en cualquier tribu de los hijos de Israel, debe casarse dentro de la familia de la tribu de su padre para que cada uno de los hijos de Israel siga poseyendo la herencia de sus antepasados,
9 Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
y así no pasará la heredad de una tribu a otra, sino las tribus de los hijos de Israel conservarán su propia herencia.
10 Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Según Yavé ordenó a Moisés, así las hijas de Zelofejad hicieron.
11 ’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
Maala, Tirsa, Hogla, Milca y Noa, hijas de Zelofejad, se casaron con los hijos de sus tíos.
12 Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
Se casaron dentro de la familia de los hijos de Manasés, hijo de José, y la heredad de ellas quedó en la tribu de la familia de su antepasado.
13 Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
Estos son los Mandamientos y las Ordenanzas que Yavé ordenó por medio de Moisés a los hijos de Israel en las llanuras de Moab, junto al Jordán, frente a Jericó.

< Ƙidaya 36 >