< Ƙidaya 36 >
1 Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
И приидоша князи племене сынов Галаадовых, сына Махирова сына Манассиина от племене сынов Иосифовых, и глаголаша пред Моисеом и пред Елеазаром жерцем и пред князи домов отечеств сынов Израилевых,
2 Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
и рекоша: господину нашему повеле Господь отдати землю наследия по жребию сыном Израилевым: и господину нашему заповеда Господь дати наследие Салпаада брата нашего дщерем его:
3 To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
и будут единому от племен сынов Израилевых в жены, и отлучится жребий их от одержания отец наших, и приложится к наследию племене, имже будут в жены, и от жребия наследия нашего отлучится:
4 Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
аще же будет оставление сынов Израилевых, и приложится наследие их к наследию племене, имже аще будут в жены, и от наследия племене отечества нашего отимется наследие их.
5 Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
И заповеда Моисей сыном Израилевым по повелению Господню, глаголя: сице племя сынов Иосифовых глаголют:
6 Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
сие слово, еже заповеда Господь дщерем Салпаадовым, глаголя: идеже угодно им, да будут в жены, токмо от сонма отечества своего да будут в жены,
7 Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
и не превратится наследие сынов Израилевых от племене в племя ино: яко кийждо в наследии племене отечества своего женитися имут сынове Израилевы:
8 Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
и всяка дщи, ужичествующая наследие от племен сынов Израилевых, единому сущих от сонма отца ея да будет жена: да ужичествуют сынове Израилевы кийждо наследие отца своего:
9 Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
и не превратится жребий от племене в племя ино, но кийждо в наследии своем да женятся сынове Израилевы.
10 Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Якоже повеле Господь Моисею, тако сотвориша дщери Салпаадовы.
11 ’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
И быша Маала и Ферса, и Егла и Мелха и Нуа, дщери Салпаадовы, сыном братии своея, от сонма Манассиина сынов Иосифовых, быша в жены:
12 Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
и бысть наследие их в племени сонма отца их.
13 Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
Сия заповеди и оправдания и суды, яже заповеда Господь рукою Моисеовою на западе Моавли при Иордане прямо Иерихону.