< Ƙidaya 36 >
1 Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
Overhodene for familiene i den ætt som nedstammet fra Gilead, en sønn av Manasses sønn Makir, og hørte til Josefs barns ætter, gikk frem for Moses og for de høvdinger som var overhoder for Israels barns familier,
2 Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
og de sa: Herren har befalt min herre å gi Israels barn landet til arv ved loddkasting, og min herre har fått befaling av Herren om å gi vår bror Selofhads arv til hans døtre.
3 To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
Men blir nu de gift med menn av Israels barns andre stammer, så går deres arv fra våre fedres arv og legges til den stammes arv som de kommer til å tilhøre, og således blir vår arvelodd mindre.
4 Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
Og når jubelåret kommer for Israels barn, så blir deres arv lagt til den stammes arv som de kommer til å tilhøre, og deres arv går fra vår fedrenestammes arv.
5 Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
Da bød Moses Israels barn efter Herrens ord og sa: Josefs barns stamme har rett i det de sier.
6 Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
Således byder Herren om Selofhads døtre: De kan gifte sig med hvem de vil, bare de gifter sig innen sin fedrenestammes ætt,
7 Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
forat ikke nogen arv hos Israels barn skal gå over fra en stamme til en annen - Israels barn skal holde fast hver ved sin fedrenestammes arv.
8 Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
Og enhver datter i Israels barns stammer som får arv, skal gifte sig med en mann av sin fedrenestammes ætt, forat Israels barn kan arve hver sine fedres arv,
9 Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
og forat ingen arv skal gå over fra en stamme til en annen, men Israels barns stammer holde fast hver ved sin arv.
10 Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Selofhads døtre gjorde således som Herren hadde befalt Moses.
11 ’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
Mahla, Tirsa og Hogla og Milka og Noa, Selofhads døtre, blev gift med sine farbrødres sønner;
12 Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
de blev gift med menn av Manasses, Josefs sønns ætter, så deres arv blev hos deres fedreneætts stamme.
13 Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
Dette er de bud og lover som Herren gav Israels barn ved Moses på Moabs ødemarker ved Jordan, midt imot Jeriko.