< Ƙidaya 36 >
1 Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
And the heads of the fathers of the families of the sons of Gilead, son of Machir, son of Manasseh, of the families of the sons of Joseph, come near, and speak before Moses, and before the princes, heads of the fathers of the sons of Israel,
2 Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
and say, Jehovah commanded my lord to give the land for inheritance by lot to the sons of Israel, and my lord hath been commanded by Jehovah to give the inheritance of Zelophehad our brother to his daughters.
3 To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
'And — they have been to one of the sons of the [other] tribes of the sons of Israel for wives, and their inheritance hath been withdrawn from the inheritance of our fathers, and hath been added to the inheritance of the tribe which is theirs, and from the lot of our inheritance it is withdrawn,
4 Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
and if it is the jubilee of the sons of Israel, then hath their inheritance been added to the inheritance of the tribe which is theirs, and from the inheritance of the tribe of our fathers is their inheritance withdrawn.'
5 Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
And Moses commandeth the sons of Israel, by the command of Jehovah, saying, 'Rightly are the tribe of the sons of Joseph speaking;
6 Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
this [is] the thing which Jehovah hath commanded concerning the daughters of Zelophehad, saying, To those good in their eyes let them be for wives; only, to a family of the tribe of their fathers let them be for wives;
7 Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
and the inheritance of the sons of Israel doth not turn round from tribe unto tribe; for each to the inheritance of the tribe of his fathers, do the sons of Israel cleave.
8 Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
'And every daughter possessing an inheritance, of the tribes of the sons of Israel, is to one of the family of the tribe of her father for a wife, so that the sons of Israel possess each the inheritance of his fathers,
9 Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
and the inheritance doth not turn round from [one] tribe to another tribe; for each to his inheritance do they cleave, the tribes of the sons of Israel.'
10 Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
As Jehovah hath commanded Moses, so have the daughters of Zelophehad done,
11 ’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
and Mahlah, Tirzah, and Hoglah, and Milcah, and Noah, daughters of Zelophehad, are to the sons of their fathers' brethren for wives;
12 Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
[to men] of the families of the sons of Manasseh, son of Joseph, they have been for wives, and their inheritance is with the tribe of the family of their father.
13 Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
These [are] the commands and the judgments which Jehovah hath commanded, by the hand of Moses, concerning the sons of Israel, in the plains of Moab, by Jordan, [near] Jericho.