< Ƙidaya 36 >

1 Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
And the heads of the fathers of the families of the sons of Gilead, son of Machir, son of Manasseh, of the families of the sons of Joseph, come near and speak before Moses and before the princes, heads of the fathers of the sons of Israel,
2 Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
and say, “YHWH commanded my lord to give the land for inheritance by lot to the sons of Israel, and my lord has been commanded by YHWH to give the inheritance of our brother Zelophehad to his daughters.
3 To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
Now [if] they have been [given] to one from the sons of the [other] tribes of the sons of Israel for wives, and their inheritance has been withdrawn from the inheritance of our fathers, and has been added to the inheritance of the tribe which is theirs, and it is withdrawn from the lot of our inheritance,
4 Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
and if it is the Jubilee of the sons of Israel, then their inheritance has been added to the inheritance of the tribe which is theirs, and their inheritance is withdrawn from the inheritance of the tribe of our fathers.”
5 Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
And Moses commands the sons of Israel by the command of YHWH, saying, “The tribe of the sons of Joseph is speaking correctly;
6 Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
this [is] the thing which YHWH has commanded concerning the daughters of Zelophehad, saying, To those good in their eyes let them be for wives; only, let them be for wives to a family of the tribe of their fathers;
7 Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
and the inheritance of the sons of Israel does not turn around from tribe to tribe; for each of the sons of Israel cleaves to the inheritance of the tribe of his fathers.
8 Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
And every daughter possessing an inheritance from the tribes of the sons of Israel is for a wife to one from the family of the tribe of her father, so that the sons of Israel each possess the inheritance of his fathers,
9 Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
and the inheritance does not turn around from [one] tribe to another tribe; for each of the tribes of the sons of Israel cleaves to his inheritance.”
10 Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
As YHWH has commanded Moses, so the daughters of Zelophehad have done,
11 ’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
and Mahlah, Tirzah, and Hoglah, and Milcah, and Noah, daughters of Zelophehad, are for wives to the sons of their fathers’ brothers;
12 Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
they have been for wives [to men] from the families of the sons of Manasseh, son of Joseph, and their inheritance is with the tribe of the family of their father.
13 Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
These [are] the commands and the judgments which YHWH has commanded by the hand of Moses concerning the sons of Israel, in the plains of Moab by the Jordan, [near] Jericho.

< Ƙidaya 36 >