< Ƙidaya 35 >

1 A filayen Mowab, wajen Urdun, ɗaura da Yeriko, Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
Gospod je spregovoril Mojzesu na moábskih ravninah, poleg Jordana, blizu Jerihe, rekoč:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su ba wa Lawiyawa garuruwan da za su zauna a ciki daga cikin gādon da Isra’ilawa za su mallaka. A kuma ba su wurin kiwo kewaye da garuruwan.
»Zapovej Izraelovim otrokom, da dajo Lévijevcem dediščino njihovih posestnih mest, da prebivajo v njih. Lévijevcem boste dali tudi predmestja za mesta okoli njih.
3 Sa’an nan za su kasance da garuruwan da za su zauna, su sami fili, da kuma za su yi kiwon garkensu na shanu da tumaki da kuma sauran dabbobinsu.
Mesta bodo imeli, da prebivajo v njih, njihova predmestja pa bodo za njihovo živino, za njihove dobrine in za vse njihove živali.
4 “Wuraren kiwo a kewayen garuruwan da za a ba wa Lawiyawa, girmansu zai zama mai fāɗin kamu dubu ɗaya daga katangar garin.
Predmestja mest, ki jih boste dali Lévijevcem, bodo segala od mestnega obzidja navzven, tisoč komolcev naokoli.
5 A bayan garin, ka auna kamu dubu biyu a wajen gabas, kamu dubu biyu a wajen yamma, kamu dubu biyu wajen kudu, da kuma kamu dubu uku wajen arewa, a bar garin a tsakiya. Za su kasance da wannan a matsayin wurin kiwo na garuruwan.
Izmerili boste mesto od zunaj, na vzhodni strani dva tisoč komolcev, na južni strani dva tisoč komolcev, na zahodni strani dva tisoč komolcev in na severni strani dva tisoč komolcev, in mesto bo v sredi. To jim bodo predmestja mest.
6 “A cikin biranen da za a ba Lawiyawa, shida daga cikin garuruwan za su zama biranen mafaka, inda wanda ya kashe mutum zai gudu yă je. Ban da wannan, a ba su waɗansu garuruwa arba’in da biyu.
Med mesti, ki jih boste dali Lévijevcem, bo tam šest mest za zatočišče, ki jih boste določili za ubijalca, da bo lahko pobegnil tja. In tem boste dodali dvainštirideset mest.
7 Duka-duka dai a ba Lawiyawa garuruwa arba’in da takwas, tare da wuraren kiwonsu.
Tako bo vseh mest, ki jih boste dali Lévijevcem, oseminštirideset mest. Te boste dali z njihovimi predmestji.
8 Garuruwan da za ku ba wa Lawiyawa daga ƙasar da Isra’ilawa suka mallaka, za a ba da su bisa girman gādon kowace kabila. Ka karɓi garuruwa masu yawa daga kabilar da take da garuruwa masu yawa, amma kaɗan daga kabilar da ba ta da garuruwa masu yawa.”
Mesta, ki jih boste dali, bodo od posesti Izraelovih otrok, od tistih, ki imajo mnogo, boste dali mnogo, toda od tistih, ki imajo malo, boste dali malo. Vsak bo od svojih mest Lévijevcem dal glede na njegovo dediščino, ki jo deduje.«
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
10 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
»Govori Izraelovim otrokom in jim reci: ›Ko boste čez Jordan prešli v kánaansko deželo,
11 ku zaɓi waɗansu garuruwan da za su zama biranen mafakarku, inda wanda ya kashe mutum cikin kuskure zai iya gudu zuwa.
potem si boste določili mesta, da bodo za vas zavetna mesta, da tja lahko pobegne ubijalec, ki nenamerno ubije katerokoli osebo.
12 Za su zama wuraren mafaka daga hannun mai bin hakki, don kada a kashe mai kisankai, tun ba a kai shi gaban shari’a, a gaban taron jama’a ba.
Ta vam bodo mesta za zatočišče pred maščevalcem, da ubijalec ne umre, dokler stoji pred skupnostjo v sodbi.
13 Waɗannan garuruwa shida da aka bayar za su zama biranen mafakarku.
Od teh mest, ki jih boste dali, boste šest mest imeli za zatočišče.
14 A ba da uku a wannan gefe na Urdun, a kuma ba da uku a Kan’ana, su zama biranen mafaka.
Dali boste tri mesta na tej strani Jordana in tri mesta v kánaanski deželi, ki bodo zavetna mesta.
15 Waɗannan garuruwa shida za su zama wurin mafaka wa Isra’ilawa, baƙi da duk sauran mutanen da suke zama a cikinsu, saboda duk wanda ya kashe mutum cikin kuskure yă iya gudu zuwa.
Teh šest mest bo zatočišče, tako za Izraelove otroke in za tujca in za začasnega prebivalca med njimi, da vsak, kdor nenamerno ubije katerokoli osebo, lahko pobegne tja.
16 “‘In wani ya bugi wani da makami na ƙarfe har ya mutu, to, shi mai kisankai ne; sai a kashe mai kisankan nan.
Če ga udari z železno pripravo, tako da ta umre, je morilec. Morilec bo zagotovo usmrčen.
17 Ko kuwa in wani yana riƙe da dutsen da ya isa yă kashe mutum a hannunsa, ya kuma harbi wani da dutsen har ya mutu, to, shi mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
Če ga udari z metom kamna, s katerim lahko umre in ta umre, je morilec. Morilec bo zagotovo usmrčen.
18 Ko kuwa wani yana da makami na itace a hannunsa da ya isa yă kashe mutum, ya kuma bugi wani da shi har ya mutu, shi ma mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
Ali če ga udari z ročnim orožjem iz lesa, s katerim ta lahko umre in ta umre, je morilec. Morilec bo zagotovo usmrčen.
19 Sai mai bin hakkin jinin yă kashe mai kisankan, sa’ad da ya sadu da mai kisankan, sai yă kashe shi.
Sam krvni maščevalec naj ubije morilca. Ko ga sreča, ga bo ubil.
20 In saboda ƙiyayya, mutum ya laɓe, ya soke wani, ko ya jefe shi da wani abu da gangan har ya mutu,
Toda če ga sune iz sovraštva ali se nanj zažene s prežanjem iz zasede, da ta umre,
21 ko kuwa saboda ƙiyayya ya naushe shi har ya mutu, sai a kashe wannan mutumin da ya yi haka; shi mai kisankai ne. Sai mai bin hakkin jini yă kashe mai kisankan in ya same shi.
ali ga v mržnji udari s svojo roko, da ta umre; kdor ga je udaril, bo zagotovo usmrčen, kajti morilec je. Krvni maščevalec naj morilca ubije, ko ga sreča.
22 “‘Amma in cikin tsautsayi ne ya soke shi, ba don ƙiyayya ba, ko kuma ya jefe shi, ba da gangan ba,
Toda če ga je nenadoma sunil brez mržnje ali je brez prežanja v zasedi nanj vrgel kakršnokoli stvar
23 ko kuwa bai gan shi ba, ya jefa dutsen da zai kashe shi a kansa, ya kuwa mutu, to, da yake shi ba abokin gābansa ba ne, bai kuma yi nufi yă ji masa ba,
ali s kakršnimkoli kamnom, s katerim lahko človek umre, pa ga ni videl in ga je vrgel nanj, da umre in ni bil njegov sovražnik niti ni iskal njegove škode,
24 dole taro su yi hukunci tsakanin mai laifin, da mai bin hakkin jini bisa waɗannan ƙa’idodi.
potem bo glede teh sodb skupnost sodila med ubijalcem in krvnim maščevalcem
25 Dole taro su kāre wanda ake zargi da kisa, daga mai bin hakkin jini. Su mai da shi birnin mafaka inda ya gudu ya tafi. Dole yă kasance a can sai mutuwar babban firist, wanda aka shafe da mai mai tsarki.
in skupnost bo ubijalca osvobodila iz roke krvnega maščevalca in skupnost ga bo vrnila v mesto njegovega zatočišča, kamor je pobegnil in ta bo ostal v njem do smrti vélikega duhovnika, ki je bil maziljen s svetim oljem.
26 “‘Amma in wanda ake zargin ya kuskura ya fita, ya kai iyakar birnin mafaka wadda ya gudu ya je,
Toda če bo ubijalec kadarkoli prišel izven meje mesta svojega zatočišča, kamor je pobegnil
27 idan mai bin hakkin jinin ya same shi a bayan gari, mai bin hakkin jinin zai iya kashe mai kisankai ɗin ba tare da wani laifi ba.
in ga krvni maščevalec najde zunaj meje mesta njegovega zatočišča in krvni maščevalec ubije ubijalca, ne bo kriv krvi,
28 Dole wanda ake zargin, yă kasance a birninsa na mafaka sai bayan mutuwa babban firist; sai bayan mutuwar babban firist ne kawai zai iya komo ga mallakarsa.
ker bi do smrti vélikega duhovnika moral ostati v mestu svojega zatočišča. Toda po smrti vélikega duhovnika se bo ubijalec lahko vrnil v deželo svoje posesti.
29 “‘Waɗannan su ne za su zama ƙa’idodin da za ku kasance da su, a dukan tsararraki masu zuwa.
Torej te stvari vam bodo za zakon sodbe skozi vaše rodove v vseh vaših prebivališčih.
30 “‘Kowa da ya kashe wani, za a kashe shi a matsayin mai kisankai, bisa ga shaidar shaidu. Amma kada a kashe wani bisa ga shaidar mutum ɗaya.
Kdorkoli ubije katerokoli osebo, bo morilec usmrčen po ustih prič. Toda ena priča ne bo pričevala zoper katerokoli osebo, da bi ji povzročila, da ta umre.
31 “‘Kada a karɓi fansa don ran wanda ya yi kisankai, wanda ya cancanci mutuwa. Lalle ne a kashe shi.
Poleg tega ne boste sprejeli nobene odkupnine za življenje morilca, ki je kriv smrti, temveč bo ta zagotovo usmrčen.
32 “‘Kada a karɓi fansa saboda wanda ya tsere zuwa birnin mafaka don yă koma yă zauna gidansa tun babban firist bai rasu ba.
Nobene odkupnine ne boste jemali za tistega, ki je pobegnil k mestu svojega zatočišča, da bi ta lahko ponovno prišel, da prebiva v deželi, do smrti duhovnika.
33 “‘Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama a ciki. Zub da jini yakan ƙazantar da ƙasa, ba a kuma iya yin kafara saboda wannan ƙasa da aka zub da jini, sai dai ta wurin jinin mutumin da ya zub da jinin.
Tako ne boste oskrunili dežele, v kateri ste, kajti kri omadežuje deželo in dežela ne more biti očiščena krvi, ki je v njej prelita, razen po krvi tistega, ki jo je prelil.
34 Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama, wadda ni kuma nake zama a ciki, gama Ni Ubangiji, ina zama a cikin Isra’ilawa.’”
Ne omadežujte torej dežele, ki jo boste poselili, v kateri prebivam, kajti jaz, Gospod, prebivam med Izraelovimi otroki.‹«

< Ƙidaya 35 >