< Ƙidaya 35 >
1 A filayen Mowab, wajen Urdun, ɗaura da Yeriko, Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
Un Tas Kungs runāja uz Mozu Moaba klajumos pie Jardānes pret Jēriku un sacīja:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su ba wa Lawiyawa garuruwan da za su zauna a ciki daga cikin gādon da Isra’ilawa za su mallaka. A kuma ba su wurin kiwo kewaye da garuruwan.
Pavēli Israēla bērniem, lai tie no savas iemantojamās daļas dod pilsētas Levitiem, kur dzīvot, un lai tie dod Levitiem arī apgabalus ārā ap viņu pilsētām.
3 Sa’an nan za su kasance da garuruwan da za su zauna, su sami fili, da kuma za su yi kiwon garkensu na shanu da tumaki da kuma sauran dabbobinsu.
Un tās pilsētas tiem būs, lai tie tur dzīvo, bet tie apgabali lai ir priekš viņu lieliem un sīkiem lopiem un priekš visiem viņu ganāmiem pulkiem.
4 “Wuraren kiwo a kewayen garuruwan da za a ba wa Lawiyawa, girmansu zai zama mai fāɗin kamu dubu ɗaya daga katangar garin.
Un tie pilsētu apgabali, ko jūs Levitiem dosiet, lai ir no pilsētas mūriem uz āru tūkstošas olektis uz visām pusēm.
5 A bayan garin, ka auna kamu dubu biyu a wajen gabas, kamu dubu biyu a wajen yamma, kamu dubu biyu wajen kudu, da kuma kamu dubu uku wajen arewa, a bar garin a tsakiya. Za su kasance da wannan a matsayin wurin kiwo na garuruwan.
Un jums būs mērot pilsētas āra pusē pret rītiem divtūkstoš olektis un pret dienas vidiem divtūkstoš olektis un pret vakariem divtūkstoš olektis un pret ziemeļiem divtūkstoš olektis, ka pilsēta ir vidū; šie būs viņiem tie pilsētu apgabali.
6 “A cikin biranen da za a ba Lawiyawa, shida daga cikin garuruwan za su zama biranen mafaka, inda wanda ya kashe mutum zai gudu yă je. Ban da wannan, a ba su waɗansu garuruwa arba’in da biyu.
Un to pilsētu starpā, ko jūs dosiet Levitiem, lai ir sešas glābšanas pilsētas, kas jums jādod, ka tas nokāvējs uz turieni bēg, un pie tām klāt viņiem būs dot vēl četrdesmit divas pilsētas.
7 Duka-duka dai a ba Lawiyawa garuruwa arba’in da takwas, tare da wuraren kiwonsu.
Visas pilsētas, ko jūs dosiet Levitiem, lai ir četrdesmit astoņas pilsētas līdz ar viņu apgabaliem.
8 Garuruwan da za ku ba wa Lawiyawa daga ƙasar da Isra’ilawa suka mallaka, za a ba da su bisa girman gādon kowace kabila. Ka karɓi garuruwa masu yawa daga kabilar da take da garuruwa masu yawa, amma kaɗan daga kabilar da ba ta da garuruwa masu yawa.”
Un no tām pilsētām, ko jūs dosiet no Israēla bērnu daļas, jums būs ņemt daudz no tiem, kam ir daudz, un maz no tiem, kam ir maz; ikvienam no savām pilsētām būs dot Levitiem pēc savas daļas, ko tas mantojis.
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Un Tas Kungs runāja uz Mozu un sacīja:
10 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
Runā uz Israēla bērniem un saki tiem: kad jūs iesiet pāri pār Jardāni uz Kanaāna zemi,
11 ku zaɓi waɗansu garuruwan da za su zama biranen mafakarku, inda wanda ya kashe mutum cikin kuskure zai iya gudu zuwa.
Tad jums būs iecelt pilsētas, kas jums lai ir par glābšanas pilsētām, ka uz turieni tas nokāvējs var bēgt, kas kādu cilvēku netīši nokāvis.
12 Za su zama wuraren mafaka daga hannun mai bin hakki, don kada a kashe mai kisankai, tun ba a kai shi gaban shari’a, a gaban taron jama’a ba.
Un šīs pilsētas lai jums ir par glābšanu no atriebēja, ka tam nokāvējam nav jāmirst, tiekams viņš nav stāvējis draudzes priekšā iztiesāšanas dēļ.
13 Waɗannan garuruwa shida da aka bayar za su zama biranen mafakarku.
Un tās pilsētas, ko jūs dosiet, lai jums ir sešas glābšanas pilsētas.
14 A ba da uku a wannan gefe na Urdun, a kuma ba da uku a Kan’ana, su zama biranen mafaka.
Trīs no šīm pilsētām noliekat viņpus Jardānes un trīs no tām pilsētām noliekat Kanaāna zemē, - glābšanas pilsētas lai tās ir.
15 Waɗannan garuruwa shida za su zama wurin mafaka wa Isra’ilawa, baƙi da duk sauran mutanen da suke zama a cikinsu, saboda duk wanda ya kashe mutum cikin kuskure yă iya gudu zuwa.
Šīs pilsētas lai Israēla bērniem ir par glābšanu, arī svešiniekam un piedzīvotājam jūsu starpā, ka uz turieni var bēgt ikviens, kas kādu cilvēku netīši nokāvis.
16 “‘In wani ya bugi wani da makami na ƙarfe har ya mutu, to, shi mai kisankai ne; sai a kashe mai kisankan nan.
Bet ja viņš to ar dzelzs ieroci sitis, ka mirst, tas ir slepkava, šim slepkavam būs tapt nokautam.
17 Ko kuwa in wani yana riƙe da dutsen da ya isa yă kashe mutum a hannunsa, ya kuma harbi wani da dutsen har ya mutu, to, shi mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
Vai ja viņš to sit ar akmeni rokā, ar ko var nokaut, tā ka mirst, tas ir slepkava, tam būs tapt nokautam.
18 Ko kuwa wani yana da makami na itace a hannunsa da ya isa yă kashe mutum, ya kuma bugi wani da shi har ya mutu, shi ma mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
Vai ja viņš to sit ar koka gabalu, ar ko var nokaut, tā ka mirst, tas ir slepkava, tam būs tapt nokautam.
19 Sai mai bin hakkin jinin yă kashe mai kisankan, sa’ad da ya sadu da mai kisankan, sai yă kashe shi.
Asiņu atriebējs lai nonāvē to slepkavu; kad tas viņu sastop, lai viņu nokauj.
20 In saboda ƙiyayya, mutum ya laɓe, ya soke wani, ko ya jefe shi da wani abu da gangan har ya mutu,
Un ja viņš nīdēdams to grūdis, vai tīši uz to ko sviedis, ka tas mirst,
21 ko kuwa saboda ƙiyayya ya naushe shi har ya mutu, sai a kashe wannan mutumin da ya yi haka; shi mai kisankai ne. Sai mai bin hakkin jini yă kashe mai kisankan in ya same shi.
Vai ja viņš nīdēdams to sitis ar savu roku, ka tas mirst, tad tam būs tapt nokautam; jo viņš ir slepkava; asiņu atriebējs lai to nokauj, kad viņu sastop.
22 “‘Amma in cikin tsautsayi ne ya soke shi, ba don ƙiyayya ba, ko kuma ya jefe shi, ba da gangan ba,
Bet ja viņš netīši bez ienaida grūdis, vai no nejauši kādu rīku uz to sviedis;
23 ko kuwa bai gan shi ba, ya jefa dutsen da zai kashe shi a kansa, ya kuwa mutu, to, da yake shi ba abokin gābansa ba ne, bai kuma yi nufi yă ji masa ba,
Vai akmenim, caur ko tas var mirt, netīši tam licis uzkrist, tā ka tas mirst, un nav bijis viņa ienaidnieks, nedz meklējis viņa nelaimi,
24 dole taro su yi hukunci tsakanin mai laifin, da mai bin hakkin jini bisa waɗannan ƙa’idodi.
Tad lai draudze tiesā starp nokāvēju un asiņu atriebēju pēc šiem likumiem.
25 Dole taro su kāre wanda ake zargi da kisa, daga mai bin hakkin jini. Su mai da shi birnin mafaka inda ya gudu ya tafi. Dole yă kasance a can sai mutuwar babban firist, wanda aka shafe da mai mai tsarki.
Un draudzei nokāvēju būs izglābt no asiņu atriebēja rokas, un draudzei būs to novest viņa glābšanas pilsētā, kurp viņš bija bēdzis, un tur tam būs palikt, kamēr augstais priesteris miris, kas ir svaidīts ar svēto eļļu.
26 “‘Amma in wanda ake zargin ya kuskura ya fita, ya kai iyakar birnin mafaka wadda ya gudu ya je,
Bet ja nokāvējs iziedams izies no savas glābšanas pilsētas robežām, kurp bija nobēdzis.
27 idan mai bin hakkin jinin ya same shi a bayan gari, mai bin hakkin jinin zai iya kashe mai kisankai ɗin ba tare da wani laifi ba.
Un asiņu atriebējs ārpus viņa glābšanas pilsētas robežām to atradīs un nokaus, tad tas nav noziedzīgs pie viņa asinīm.
28 Dole wanda ake zargin, yă kasance a birninsa na mafaka sai bayan mutuwa babban firist; sai bayan mutuwar babban firist ne kawai zai iya komo ga mallakarsa.
Jo tam bija jāpaliek savā glābšanas pilsētā, kamēr augstais priesteris nomirs; bet pēc tā augstā priestera miršanas nokāvējs lai griežas atpakaļ uz savu zemes daļu.
29 “‘Waɗannan su ne za su zama ƙa’idodin da za ku kasance da su, a dukan tsararraki masu zuwa.
Un tas lai jums ir par tiesas likumu pie jūsu pēcnākamiem visās jūsu māju vietās.
30 “‘Kowa da ya kashe wani, za a kashe shi a matsayin mai kisankai, bisa ga shaidar shaidu. Amma kada a kashe wani bisa ga shaidar mutum ɗaya.
Ja kas kādu cilvēku nosit, tad uz liecinieku vārdu slepkavam būs tapt nokautam, bet vienam lieciniekam vien nebūs liecību dot pret kādu cilvēku, ka tam būtu jāmirst.
31 “‘Kada a karɓi fansa don ran wanda ya yi kisankai, wanda ya cancanci mutuwa. Lalle ne a kashe shi.
Tev arī nebūs ņemt atpirkšanas maksu par slepkavu, kas nāvi pelnījis, jo tam būs tapt nokautam.
32 “‘Kada a karɓi fansa saboda wanda ya tsere zuwa birnin mafaka don yă koma yă zauna gidansa tun babban firist bai rasu ba.
Jums arī nebūs ņemt atpirkšanas maksu par to, kas savā glābšanas pilsētā ir nobēdzis, ka tas atkal nāktu dzīvot savā zemes daļā, pirms augstais priesteris miris.
33 “‘Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama a ciki. Zub da jini yakan ƙazantar da ƙasa, ba a kuma iya yin kafara saboda wannan ƙasa da aka zub da jini, sai dai ta wurin jinin mutumin da ya zub da jinin.
Un jums nebūs sagānīt to zemi, kur jūs esat; jo tās tādas asinis sagāna to zemi, un to zemi nevar salīdzināt to asiņu dēļ, kas tur izlietas, kā vien caur tā asinīm, kas tās izlējis.
34 Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama, wadda ni kuma nake zama a ciki, gama Ni Ubangiji, ina zama a cikin Isra’ilawa.’”
Tad nu nesagāniet to zemi, kur jūs dzīvojat, un kur Mans dzīvoklis, jo Es esmu Tas Kungs, kas dzīvo Israēla bērnu vidū.