< Ƙidaya 35 >
1 A filayen Mowab, wajen Urdun, ɗaura da Yeriko, Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
Yahweh spoke to Moses on the plains of Moab by the Jordan at Jericho and said,
2 “Ka umarci Isra’ilawa su ba wa Lawiyawa garuruwan da za su zauna a ciki daga cikin gādon da Isra’ilawa za su mallaka. A kuma ba su wurin kiwo kewaye da garuruwan.
“Command the people of Israel to give some of their own shares of land to the Levites. They must give them cities to live in and pastureland surrounding those cities.
3 Sa’an nan za su kasance da garuruwan da za su zauna, su sami fili, da kuma za su yi kiwon garkensu na shanu da tumaki da kuma sauran dabbobinsu.
The Levites will have these cities to live in. The pastureland will be for their cattle, their flocks, and all their animals.
4 “Wuraren kiwo a kewayen garuruwan da za a ba wa Lawiyawa, girmansu zai zama mai fāɗin kamu dubu ɗaya daga katangar garin.
The pasturelands around the cities that you will give to the Levites must extend from the city walls for one thousand cubits in every direction.
5 A bayan garin, ka auna kamu dubu biyu a wajen gabas, kamu dubu biyu a wajen yamma, kamu dubu biyu wajen kudu, da kuma kamu dubu uku wajen arewa, a bar garin a tsakiya. Za su kasance da wannan a matsayin wurin kiwo na garuruwan.
You must measure two thousand cubits from outside the city on the east side, and two thousand cubits to the south side, two thousand cubits to the west side, and two thousand cubits to the north side. This will be the pasturelands for their cities. The cities will be in the center.
6 “A cikin biranen da za a ba Lawiyawa, shida daga cikin garuruwan za su zama biranen mafaka, inda wanda ya kashe mutum zai gudu yă je. Ban da wannan, a ba su waɗansu garuruwa arba’in da biyu.
Six of the cities that you will give to Levites must serve as cities of refuge. You must provide these as places to which a person who has killed someone can flee. Also provide forty-two other cities.
7 Duka-duka dai a ba Lawiyawa garuruwa arba’in da takwas, tare da wuraren kiwonsu.
The cities that you give to the Levites will total forty-eight. You must give their pasturelands with them.
8 Garuruwan da za ku ba wa Lawiyawa daga ƙasar da Isra’ilawa suka mallaka, za a ba da su bisa girman gādon kowace kabila. Ka karɓi garuruwa masu yawa daga kabilar da take da garuruwa masu yawa, amma kaɗan daga kabilar da ba ta da garuruwa masu yawa.”
The larger tribes of the people of Israel, the tribes that have more land, must provide more cities. The smaller tribes will provide fewer cities. Each tribe must provide for the Levites according to the share that it has received.”
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Then Yahweh spoke to Moses and said,
10 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
“Speak to the people of Israel and say to them, 'When you cross over the Jordan into the land of Canaan,
11 ku zaɓi waɗansu garuruwan da za su zama biranen mafakarku, inda wanda ya kashe mutum cikin kuskure zai iya gudu zuwa.
then you must choose cities to serve as cities of refuge for you, a place to which a person who has killed someone unintentionally may flee.
12 Za su zama wuraren mafaka daga hannun mai bin hakki, don kada a kashe mai kisankai, tun ba a kai shi gaban shari’a, a gaban taron jama’a ba.
These cities must be your refuge from the avenger, so that the accused man will not be killed without first standing trial before the community.
13 Waɗannan garuruwa shida da aka bayar za su zama biranen mafakarku.
You must choose six cities as cities of refuge.
14 A ba da uku a wannan gefe na Urdun, a kuma ba da uku a Kan’ana, su zama biranen mafaka.
You must provide three cities beyond the Jordan and three in the land of Canaan. They will be cities of refuge.
15 Waɗannan garuruwa shida za su zama wurin mafaka wa Isra’ilawa, baƙi da duk sauran mutanen da suke zama a cikinsu, saboda duk wanda ya kashe mutum cikin kuskure yă iya gudu zuwa.
For the people of Israel, for the foreigners, for anyone living among you, these six cities will serve as a refuge to which anyone who kills someone unintentionally can flee.
16 “‘In wani ya bugi wani da makami na ƙarfe har ya mutu, to, shi mai kisankai ne; sai a kashe mai kisankan nan.
But if an accused man has struck his victim with an instrument of iron, and if his victim dies, then the accused is indeed a murderer. He must certainly be put to death.
17 Ko kuwa in wani yana riƙe da dutsen da ya isa yă kashe mutum a hannunsa, ya kuma harbi wani da dutsen har ya mutu, to, shi mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
If an accused man has struck his victim with a stone in his hand that might kill the victim, and if his victim dies, then the accused is indeed a murderer. He must certainly be put to death.
18 Ko kuwa wani yana da makami na itace a hannunsa da ya isa yă kashe mutum, ya kuma bugi wani da shi har ya mutu, shi ma mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
If an accused man has struck his victim with a wooden weapon that might kill the victim, and if the victim dies, then the accused is indeed a murderer. He must certainly be put to death.
19 Sai mai bin hakkin jinin yă kashe mai kisankan, sa’ad da ya sadu da mai kisankan, sai yă kashe shi.
The avenger of blood may put the murderer to death. When he meets him, the avenger of blood must put him to death.
20 In saboda ƙiyayya, mutum ya laɓe, ya soke wani, ko ya jefe shi da wani abu da gangan har ya mutu,
If he strikes another in hatred or throws something at him, while hiding to ambush him, so that the victim dies,
21 ko kuwa saboda ƙiyayya ya naushe shi har ya mutu, sai a kashe wannan mutumin da ya yi haka; shi mai kisankai ne. Sai mai bin hakkin jini yă kashe mai kisankan in ya same shi.
or if he strikes him down in hatred with his hand so that the victim dies, then the accused who struck him must surely be put to death. He is a murderer. The avenger of blood may put the murderer to death when he meets him.
22 “‘Amma in cikin tsautsayi ne ya soke shi, ba don ƙiyayya ba, ko kuma ya jefe shi, ba da gangan ba,
But if an accused man suddenly hits a victim without premeditated hate or throws something that hits the victim without lying in wait
23 ko kuwa bai gan shi ba, ya jefa dutsen da zai kashe shi a kansa, ya kuwa mutu, to, da yake shi ba abokin gābansa ba ne, bai kuma yi nufi yă ji masa ba,
or if he throws a stone that could kill a victim without seeing the victim, then the accused was not the victim's enemy; he was not trying to hurt the victim. But this is what to do if the victim dies anyway.
24 dole taro su yi hukunci tsakanin mai laifin, da mai bin hakkin jini bisa waɗannan ƙa’idodi.
In that case, the community must judge between the accused and the avenger of blood on the basis of these rules.
25 Dole taro su kāre wanda ake zargi da kisa, daga mai bin hakkin jini. Su mai da shi birnin mafaka inda ya gudu ya tafi. Dole yă kasance a can sai mutuwar babban firist, wanda aka shafe da mai mai tsarki.
The community must rescue the accused from the power of the avenger of blood. The community must return the accused to the city of refuge to which he had originally fled. He must live there until the death of the current high priest, the one who was anointed with the holy oil.
26 “‘Amma in wanda ake zargin ya kuskura ya fita, ya kai iyakar birnin mafaka wadda ya gudu ya je,
But if the accused man at any time goes beyond the border of the city of refuge to which he fled,
27 idan mai bin hakkin jinin ya same shi a bayan gari, mai bin hakkin jinin zai iya kashe mai kisankai ɗin ba tare da wani laifi ba.
and if the avenger of blood finds him outside the border of his city of refuge, and if he kills the accused man, the avenger of blood will not be guilty of murder.
28 Dole wanda ake zargin, yă kasance a birninsa na mafaka sai bayan mutuwa babban firist; sai bayan mutuwar babban firist ne kawai zai iya komo ga mallakarsa.
This is because the accused man should have remained in his city of refuge until the death of the high priest. After the death of the high priest, the accused may return to the land where he has his own property.
29 “‘Waɗannan su ne za su zama ƙa’idodin da za ku kasance da su, a dukan tsararraki masu zuwa.
These laws must be statutes for you through all your people's generations in all the places where you live.
30 “‘Kowa da ya kashe wani, za a kashe shi a matsayin mai kisankai, bisa ga shaidar shaidu. Amma kada a kashe wani bisa ga shaidar mutum ɗaya.
Whoever kills any person, the murderer must be killed, as testified to by the words of witnesses. But one witness' word alone may not cause any person to be put to death.
31 “‘Kada a karɓi fansa don ran wanda ya yi kisankai, wanda ya cancanci mutuwa. Lalle ne a kashe shi.
Also, you must not accept ransom for the life of a murderer who is guilty of murder. He must certainly be put to death.
32 “‘Kada a karɓi fansa saboda wanda ya tsere zuwa birnin mafaka don yă koma yă zauna gidansa tun babban firist bai rasu ba.
You must not accept ransom for the one who has fled to a city of refuge. You must not in this way allow him to reside on his own property until the high priest dies.
33 “‘Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama a ciki. Zub da jini yakan ƙazantar da ƙasa, ba a kuma iya yin kafara saboda wannan ƙasa da aka zub da jini, sai dai ta wurin jinin mutumin da ya zub da jinin.
Do not pollute in this way the land where you live, because blood from murder pollutes the land. No atonement can be made for the land when blood has been shed on it, except by the blood of the one who shed it.
34 Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama, wadda ni kuma nake zama a ciki, gama Ni Ubangiji, ina zama a cikin Isra’ilawa.’”
So you must not defile the land in which you live because I am living in it. I, Yahweh, live among the people of Israel.'”