< Ƙidaya 35 >

1 A filayen Mowab, wajen Urdun, ɗaura da Yeriko, Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
And the Lord spoke to Moses to the west of Moab by Jordan near Jericho, saying,
2 “Ka umarci Isra’ilawa su ba wa Lawiyawa garuruwan da za su zauna a ciki daga cikin gādon da Isra’ilawa za su mallaka. A kuma ba su wurin kiwo kewaye da garuruwan.
Give orders to the children of Israel, and they shall give to the Levites cities to dwell in from the lot of their possession, and they shall give to the Levites the suburbs of the cities round about them.
3 Sa’an nan za su kasance da garuruwan da za su zauna, su sami fili, da kuma za su yi kiwon garkensu na shanu da tumaki da kuma sauran dabbobinsu.
And the cities shall be for them to dwell in, and their enclosures shall be for their cattle and all their beasts.
4 “Wuraren kiwo a kewayen garuruwan da za a ba wa Lawiyawa, girmansu zai zama mai fāɗin kamu dubu ɗaya daga katangar garin.
And the suburbs of the cities which ye shall give to the Levites, shall be from the wall of the city and outwards two thousand cubits round about.
5 A bayan garin, ka auna kamu dubu biyu a wajen gabas, kamu dubu biyu a wajen yamma, kamu dubu biyu wajen kudu, da kuma kamu dubu uku wajen arewa, a bar garin a tsakiya. Za su kasance da wannan a matsayin wurin kiwo na garuruwan.
And thou shalt measure outside the city on the east side two thousand cubits, and on the south side two thousand cubits, and on the west side two thousand cubits, and on the north side two thousand cubits; and your city shall be in the midst of this, and the suburbs of the cities [as described].
6 “A cikin biranen da za a ba Lawiyawa, shida daga cikin garuruwan za su zama biranen mafaka, inda wanda ya kashe mutum zai gudu yă je. Ban da wannan, a ba su waɗansu garuruwa arba’in da biyu.
And ye shall give the cities to the Levites, the six cities of refuge which ye shall give for the slayer to flee thither, and in addition to these, forty-two cities.
7 Duka-duka dai a ba Lawiyawa garuruwa arba’in da takwas, tare da wuraren kiwonsu.
Ye shall give to the Levites in all forty-eight cities, them and their suburbs.
8 Garuruwan da za ku ba wa Lawiyawa daga ƙasar da Isra’ilawa suka mallaka, za a ba da su bisa girman gādon kowace kabila. Ka karɓi garuruwa masu yawa daga kabilar da take da garuruwa masu yawa, amma kaɗan daga kabilar da ba ta da garuruwa masu yawa.”
And as for the cities which ye shall give out of the possession of the children of Israel, from those [that have] much [ye shall give] much, and from those that have less ye shall give less: they shall give of their cities to the Levites each one according to his inheritance which they shall inherit.
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying,
10 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
Speak to the children of Israel, and thou shalt say to them, Ye are to cross over Jordan into the land of Chanaan.
11 ku zaɓi waɗansu garuruwan da za su zama biranen mafakarku, inda wanda ya kashe mutum cikin kuskure zai iya gudu zuwa.
And ye shall appoint to yourselves cities: they shall be to you cities of refuge for the slayer to flee to, every one who has killed another unintentionally.
12 Za su zama wuraren mafaka daga hannun mai bin hakki, don kada a kashe mai kisankai, tun ba a kai shi gaban shari’a, a gaban taron jama’a ba.
And the cities shall be to you places of refuge from the avenger of blood, and the slayer shall not die until he stands before the congregation for judgment.
13 Waɗannan garuruwa shida da aka bayar za su zama biranen mafakarku.
And the cities which ye shall assign, [even] the six cities, shall be places of refuge for you.
14 A ba da uku a wannan gefe na Urdun, a kuma ba da uku a Kan’ana, su zama biranen mafaka.
Ye shall assign three cities on the other side of Jordan, and ye shall assign three cities in the land of Chanaan.
15 Waɗannan garuruwa shida za su zama wurin mafaka wa Isra’ilawa, baƙi da duk sauran mutanen da suke zama a cikinsu, saboda duk wanda ya kashe mutum cikin kuskure yă iya gudu zuwa.
It shall be a place of refuge for the children of Israel, and for the stranger, and for him that sojourns among you; these cities shall be for a place of refuge, for every one to flee thither who has killed a man unintentionally.
16 “‘In wani ya bugi wani da makami na ƙarfe har ya mutu, to, shi mai kisankai ne; sai a kashe mai kisankan nan.
And if he should smite him with an iron instrument, and the man should die, he is a murderer; let the murderer by all means be put to death.
17 Ko kuwa in wani yana riƙe da dutsen da ya isa yă kashe mutum a hannunsa, ya kuma harbi wani da dutsen har ya mutu, to, shi mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
And if he should smite him with a stone [thrown] from his hand, whereby a man may die, and he [thus] die, he is a murderer; let the murderer by all means be put to death.
18 Ko kuwa wani yana da makami na itace a hannunsa da ya isa yă kashe mutum, ya kuma bugi wani da shi har ya mutu, shi ma mai kisankai ne, sai a kashe mai kisankan nan.
And if he should smite him with an instrument of wood from his hand, whereby he may die, and he [thus] die, he is a murderer; let the murderer by all means be put to death.
19 Sai mai bin hakkin jinin yă kashe mai kisankan, sa’ad da ya sadu da mai kisankan, sai yă kashe shi.
The avenger of blood himself shall slay the murderer: whensoever he shall meet him he shall slay him.
20 In saboda ƙiyayya, mutum ya laɓe, ya soke wani, ko ya jefe shi da wani abu da gangan har ya mutu,
And if he should thrust him through enmity, or cast any thing upon him from an ambuscade, and the man should die,
21 ko kuwa saboda ƙiyayya ya naushe shi har ya mutu, sai a kashe wannan mutumin da ya yi haka; shi mai kisankai ne. Sai mai bin hakkin jini yă kashe mai kisankan in ya same shi.
or if he have smitten him with his hand through anger, and the man should die, let the man that smote him be put to death by all means, he is a murderer: let the murderer by all means be put to death: the avenger of blood shall slay the murderer when he meets him.
22 “‘Amma in cikin tsautsayi ne ya soke shi, ba don ƙiyayya ba, ko kuma ya jefe shi, ba da gangan ba,
But if he should thrust him suddenly, not through enmity, or cast any thing upon him, not from an ambuscade,
23 ko kuwa bai gan shi ba, ya jefa dutsen da zai kashe shi a kansa, ya kuwa mutu, to, da yake shi ba abokin gābansa ba ne, bai kuma yi nufi yă ji masa ba,
or [smite him] with any stone, whereby a man may die, unawares, and it should fall upon him, and he should die, but he was not his enemy, nor sought to hurt him;
24 dole taro su yi hukunci tsakanin mai laifin, da mai bin hakkin jini bisa waɗannan ƙa’idodi.
then the assembly shall judge between the smiter and the avenger of blood, according to these judgments.
25 Dole taro su kāre wanda ake zargi da kisa, daga mai bin hakkin jini. Su mai da shi birnin mafaka inda ya gudu ya tafi. Dole yă kasance a can sai mutuwar babban firist, wanda aka shafe da mai mai tsarki.
And the congregation shall rescue the slayer from the avenger of blood, and the congregation shall restore him to his city of refuge, whither he fled for refuge; and he shall dwell there till the death of the high-priest, whom they anointed with the holy oil.
26 “‘Amma in wanda ake zargin ya kuskura ya fita, ya kai iyakar birnin mafaka wadda ya gudu ya je,
But if the slayer should in any wise go out beyond the bounds of the city whither he fled for refuge,
27 idan mai bin hakkin jinin ya same shi a bayan gari, mai bin hakkin jinin zai iya kashe mai kisankai ɗin ba tare da wani laifi ba.
and the avenger of blood should find him without the bounds of the city of his refuge, and the avenger of blood should kill the slayer, he is not guilty.
28 Dole wanda ake zargin, yă kasance a birninsa na mafaka sai bayan mutuwa babban firist; sai bayan mutuwar babban firist ne kawai zai iya komo ga mallakarsa.
For he ought to have remained in the city of refuge till the high-priest died; and after the death of the high-priest the slayer shall return to the land of his possession.
29 “‘Waɗannan su ne za su zama ƙa’idodin da za ku kasance da su, a dukan tsararraki masu zuwa.
And these things shall be to you for an ordinance of judgment throughout your generations in all your dwellings.
30 “‘Kowa da ya kashe wani, za a kashe shi a matsayin mai kisankai, bisa ga shaidar shaidu. Amma kada a kashe wani bisa ga shaidar mutum ɗaya.
Whoever kills a man, thou shalt slay the murderer on the testimony of witnesses; and one witness shall not testify against a soul that he should die.
31 “‘Kada a karɓi fansa don ran wanda ya yi kisankai, wanda ya cancanci mutuwa. Lalle ne a kashe shi.
And ye shall not accept ransoms for life from a murderer who is worthy of death, for he shall be surely put to death.
32 “‘Kada a karɓi fansa saboda wanda ya tsere zuwa birnin mafaka don yă koma yă zauna gidansa tun babban firist bai rasu ba.
Ye shall not accept a ransom [to excuse] his fleeing to the city of refuge, so that he should again dwell in the land, until the death of the high-priest.
33 “‘Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama a ciki. Zub da jini yakan ƙazantar da ƙasa, ba a kuma iya yin kafara saboda wannan ƙasa da aka zub da jini, sai dai ta wurin jinin mutumin da ya zub da jinin.
So shall ye not pollute with murder the land in which ye dwell; for this blood pollutes the land, and the land shall not be purged from the blood shed upon it, but by the blood of him that shed it.
34 Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama, wadda ni kuma nake zama a ciki, gama Ni Ubangiji, ina zama a cikin Isra’ilawa.’”
And ye shall not defile the land whereon ye dwell, on which I dwell in the midst of you; for I am the Lord dwelling in the midst of the children of Israel.

< Ƙidaya 35 >