< Ƙidaya 34 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
El Señor le dijo a Moisés,
2 “Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
“Dales esta orden a los israelitas: Cuando entren en el país de Canaán, se les asignarán las posesiones con los siguientes límites:
3 “‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
“La extensión sur de su país será desde el desierto de Zin a lo largo de la frontera de Edom. Su frontera sur correrá hacia el este desde el final del Mar Muerto,
4 tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
cruzará al sur del Paso del Escorpión, hasta Zin, y alcanzará su límite sur al sur de Cades-barnea. Luego irá a Hazar-addar y a Azmon.
5 inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
Allí la frontera girará desde Azmon hasta el Wadi de Egipto, terminando en el Mar Mediterráneo.
6 “‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
“Su frontera occidental será la costa del Mar Mediterráneo. Este será su límite al oeste.
7 “‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
“Tu frontera norte irá desde el Mar Mediterráneo hasta el Monte Hor.
8 za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
Desde el Monte Hor la frontera irá a Lebo-hamat, luego a Zedad,
9 tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
a Zifrón, terminando en Hazar-enan. Este será su límite al norte.
10 “‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
“Su frontera oriental irá directamente de Hazar-enan a Sefan.
11 Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
Luego la frontera bajará de Sefam a Ribla en el lado este de Aín. Pasará a lo largo de las laderas al este del Mar de Galilea.
12 Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
Luego el límite bajará a lo largo del Jordán, terminando en el Mar Muerto. Esta será su tierra con sus fronteras circundantes”.
13 Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
Moisés dio la orden a los israelitas, “Asignen la propiedad de esta tierra por sorteo. El Señor ha ordenado que sea entregada a las nueve tribus y media.
14 saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
Las tribus de Rubén y Gad, junto con la media tribu de Manasés, ya han recibido su asignación.
15 Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
Estas dos tribus y media han recibido su asignación en el lado este del Jordán, frente a Jericó”.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
El Señor le dijo a Moisés,
17 “Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
“Estos son los nombres de los hombres que se encargarán de asignar la propiedad de la tierra para ustedes: Eleazar el sacerdote y Josué, hijo de Nun.
18 Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
Que un líder de cada tribu ayude en la distribución de la tierra.
19 “Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
Estos son sus nombres: “De la tribu de Judá: Caleb, hijo de Jefone.
20 Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
De la tribu de Simeón: Semuel, hijo de Amiud.
21 Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
De la tribu de Benjamín: Elidad, hijo de Quislón.
22 Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
Un líder de la tribu de Dan: Buqui, hijo de Jogli.
23 Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
Un líder de la tribu de Manasés, hijo de José: Haniel, hijo de Efod.
24 Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
Un líder de la tribu de Efraín: Kemuel, hijo de Siftán.
25 Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
Un líder de la tribu de Zabulón: Eli-zafán, hijo de Parnac.
26 Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
Un líder de la tribu de Isacar: Paltiel, hijo de Azán.
27 Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
Un líder de la tribu de Aser: Ahiud, hijo de Selomi.
28 Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
Un líder de la tribu de Neftalí: Pedael, hijo de Amiud”.
29 Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.
Estos son los nombres de los que el Señor puso a cargo de la asignación de la propiedad de la tierra en el país de Canaán.

< Ƙidaya 34 >