< Ƙidaya 34 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Und der Herr sprach zu Moses:
2 “Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
"Befiehl den Söhnen Israels und sprich zu ihnen: Kommt ihr in das Land Kanaan, dann ist dies das Land, das euch als Eigentum zufällt, das Land Kanaan nach seinen Grenzen.
3 “‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
Der Südsaum sei euch von der Wüste Sin an Edom entlang, und zwar sei euch Südgrenze das Ende des Salzmeeres im Osten.
4 tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
Dann wende sich euch die Grenze südlich von der Skorpionensteige und gehe weiter nach Sin hinüber, bis sie südlich von Kades Barnea endet! Dann laufe sie nach Chasar Addar aus und gehe weiter nach Asmon!
5 inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
Die Grenze wende sich von Asmon zum Bach Ägyptens, bis sie am Meer endet!
6 “‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
Westgrenze sei euch das große Meer und seine Küste! Das soll eure Westgrenze sein!
7 “‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
Nordgrenze soll euch dies sein: Vom großen Meere sollt ihr sie euch bis zum Berge Hor ziehen!
8 za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
Vom Berge Hor sollt ihr sie euch bis Chamat ziehen! Endpunkt der Grenze sei Sedad!
9 tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
Dann laufe die Grenze nach Siphron und weiter bis Chasar Enan als ihrem Endpunkt! Dies soll eure Nordgrenze sein!
10 “‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
Als Ostgrenze setzet euch fest die Strecke von Chasar Enan bis Sepham!
11 Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
Die Grenze senke sich von Sepham nach Rebel, östlich von Ain! Dann senke sich die Grenze und stoße auf den Bergrücken östlich vom See Genesareth!
12 Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
Dann senke sich die Grenze an den Jordan, bis sie am Salzmeer endet! Das sollen ringsum des Landes Grenzen sein!'"
13 Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
Und Moses gebot den Israeliten: "Das ist das Land, das ihr euch durch das Los zueignen sollt und das der Herr den neuneinhalb Stämmen zu geben befohlen hat."
14 saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
Denn die Familien des Stammes der Rubensöhne und die Familie des Stammes der Gadsöhne und der halbe Stamm Manasse hatten ihren Besitz schon erhalten.
15 Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
Die zweieinhalb Stämme hatten ihren Besitz jenseits des Jordan, auf der Ostseite des Jordan bei Jericho erhalten.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
Und der Herr sprach zu Moses:
17 “Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
"Dies sind die Namen der Männer, die euch das Land zuteilen sollen: der Priester Eleazar und Josue, des Nun Sohn.
18 Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
Zieht von jedem Stamme je einen Fürsten bei der Landesverteilung hinzu!
19 “Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
Dies sind die Namen der Männer: vom Stamme Juda Kaleb, Jephunnes Sohn,
20 Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
vom Stamme der Simeonsöhne Semuel, Ammihuds Sohn,
21 Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
vom Stamme Benjamin Elidad, Kislons Sohn,
22 Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
vom Stamme der Dansöhne als Fürst Bukki, Joglis Sohn,
23 Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
von den Josephsöhnen, vom Stamme der Manassesöhne, als Fürst Channiel, Ephods Sohn,
24 Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
vom Stamme der Ephraimsöhne als Fürst Kemuel, Siphtans Sohn,
25 Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
vom Stamme der Zabulonsöhne als Fürst Elisaphan, Parnaks Sohn,
26 Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
vom Stamme der Issakarsöhne als Fürst Paltiel, Azzans Sohn,
27 Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
vom Stamme der Assersöhne als Fürst Achihud, Selomis Sohn,
28 Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
von Stamme der Naphtalisöhne, als Fürst Pedahel, Ammihuds Sohn.
29 Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.
Das sind die, denen der Herr befohlen, den Israeliten im Lande Kanaan ihren Besitz auszuteilen."