< Ƙidaya 34 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
L'Éternel parla encore à Moïse, en disant:
2 “Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
Ordonne ceci aux enfants d'Israël, et dis-leur: Lorsque vous serez entrés au pays de Canaan, ce pays qui vous échoit en héritage, le pays de Canaan selon ses limites,
3 “‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
La région du Midi sera à vous depuis le désert de Tsin, le long d'Édom. Ainsi votre frontière du Midi partira du bout de la mer Salée, vers l'Orient.
4 tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
Et cette frontière tournera au midi de la montée d'Akrabbim, passera vers Tsin, et aboutira au midi de Kadès-Barnéa; puis elle sortira vers Hatsar-Addar, et passera vers Atsmon.
5 inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
D'Atsmon la frontière tournera vers le torrent d'Égypte, et aboutira à la mer.
6 “‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
Et quant à la frontière d'Occident, vous aurez la grande mer pour limite; ce sera votre frontière occidentale.
7 “‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
Et voici quelle sera votre frontière du Nord: depuis la grande mer vous marquerez pour vos limites la montagne de Hor;
8 za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
Puis de la montagne de Hor, vous marquerez pour vos limites l'entrée de Hamath, et la frontière aboutira à Tsedad.
9 tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
Et cette frontière sortira vers Ziphron, et aboutira à Hatsar-Enan; telle sera votre frontière du Nord.
10 “‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
Puis vous prendrez pour vos frontières, vers l'Orient, de Hatsar-Enan à Shepham.
11 Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
Et la frontière descendra de Shepham à Ribla, à l'Orient d'Aïn; puis cette frontière descendra et atteindra la côte de la mer de Kinnéreth, vers l'Orient;
12 Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
Enfin la frontière descendra vers le Jourdain, et aboutira à la mer Salée. Tel sera le pays que vous aurez, selon ses frontières tout autour.
13 Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
Et Moïse commanda aux enfants d'Israël, et leur dit: C'est là le pays que vous partagerez par le sort, et que l'Éternel a commandé de donner aux neuf tribus et à la moitié d'une tribu.
14 saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
Car la tribu des descendants de Ruben, selon les maisons de leurs pères, et la tribu des descendants de Gad, selon les maisons de leurs pères, et la demi-tribu de Manassé ont reçu leur héritage.
15 Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
Ces deux tribus et la demi-tribu ont reçu leur héritage de ce côté-ci du Jourdain de Jérico, à l'Orient, vers le Levant.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
L'Éternel parla encore à Moïse, en disant:
17 “Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
Voici les noms des hommes qui vous partageront le pays: Éléazar, le sacrificateur, et Josué, fils de Nun.
18 Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
Vous prendrez aussi un chef de chaque tribu, pour partager le pays.
19 “Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
Voici les noms de ces hommes: Pour la tribu de Juda, Caleb, fils de Jéphunné;
20 Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
Pour la tribu des enfants de Siméon, Samuël, fils d'Ammihud;
21 Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
Pour la tribu des enfants de Benjamin, Élidad, fils de Kislon;
22 Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
Pour la tribu des enfants de Dan, un chef, Buki, fils de Jogli;
23 Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
Pour les enfants de Joseph: pour la tribu des enfants de Manassé, un chef, Hanniel, fils d'Éphod;
24 Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
Et pour la tribu des enfants d'Éphraïm, un chef, Kemuël, fils de Shiphtan;
25 Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
Pour la tribu des enfants de Zabulon, un chef, Élitsaphan, fils de Parnac;
26 Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
Pour la tribu des enfants d'Issacar, un chef, Paltiel, fils d'Azzan;
27 Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
Pour la tribu des enfants d'Asser, un chef, Ahihud, fils de Shelomi;
28 Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
Et pour la tribu des enfants de Nephthali, un chef, Pedahel, fils d'Ammihud.
29 Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.
Tels sont ceux auxquels l'Éternel commanda de partager l'héritage aux enfants d'Israël, dans le pays de Canaan.

< Ƙidaya 34 >