< Ƙidaya 34 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
2 “Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
Commande aux enfants d'Israël, et leur dis: Parce que vous allez entrer au pays de Canaan, ce [sera] ici le pays qui vous écherra en héritage, le pays de Canaan selon ses limites.
3 “‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
Votre frontière du côté du Midi sera depuis le désert de Tsin, le long d'Edom; tellement que votre frontière du côté du Midi commencera au bout de la mer Salée vers l'Orient.
4 tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
Et cette frontière tournera du Midi vers la montée de Hakrabbim, et passera jusqu'à Tsin; et elle aboutira du côté du Midi, à Kadès-barné, et sortira aussi en Hatsar-addar, et passera jusqu'à Hatsmon.
5 inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
Et cette frontière tournera depuis Hatsmon jusqu'au torrent d'Egypte; et elle aboutira à la mer.
6 “‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
Et quant à la frontière d'Occident, vous aurez la grande mer, et ses limites; ce vous sera la frontière Occidentale.
7 “‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
Et ce sera [ici] votre frontière du Septentrion; depuis la grande mer vous marquerez pour vos limites la montagne de Hor.
8 za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
Et de la montagne de Hor vous marquerez pour vos limites l'entrée de Hamath; et cette frontière se rendra vers Tsédad.
9 tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
Et cette frontière passera jusqu'à Ziphron, et elle aboutira à Hatsar-hénan; telle sera votre frontière du Septentrion.
10 “‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
Puis vous marquerez pour vos limites vers l'Orient depuis Hatsar-hénan vers Sepham.
11 Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
Et cette frontière descendra de Sepham à Riblat, du côté de l'Orient de Hajin; et cette frontière descendra et s'étendra le long de la mer de Kinnereth vers l'Orient.
12 Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
Et cette frontière descendra au Jourdain, et se rendra à la mer salée; tel sera le pays que vous aurez selon ses limites tout autour.
13 Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
Et Moïse commanda aux enfants d'Israël, en disant: C'est là le pays que vous hériterez par sort, lequel l'Eternel a commandé de donner à neuf Tribus, et à la moitié d'une Tribu.
14 saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
Car la Tribu des enfants de Ruben selon les familles de leurs pères, et la Tribu des enfants de Gad, selon les familles de leurs pères, ont pris leur héritage; [et] la demi-Tribu de Manassé a pris aussi son héritage.
15 Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
Deux tribus, [dis-je], et la moitié d'une Tribu, ont pris leur héritage au deçà du Jourdain de Jéricho, du côté du Levant.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
17 “Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
Ce sont ici les noms des hommes qui vous partageront le pays, Eléazar, le Sacrificateur, et Josué, fils de Nun.
18 Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
Vous prendrez aussi un des principaux de chaque Tribu pour faire le partage du pays.
19 “Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
Et ce sont ici les noms de ces hommes-là. Pour la Tribu de Juda, Caleb, fils de Jéphunné.
20 Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
Pour la Tribu des enfants de Siméon, Samuel, fils de Hammiud.
21 Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
Pour la Tribu de Benjamin, Elidad, fils de Kislon.
22 Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
Pour la Tribu des enfants de Dan, celui qui en est le chef, Bukki, fils de Jogli.
23 Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
Des enfants de Joseph, pour la Tribu des enfants de Manassé, celui qui en est le chef, Hanniel, fils d'Ephod.
24 Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
Pour la Tribu des enfants d'Ephraïm, celui qui en est le chef, Kémuel, fils de Siphthan.
25 Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
Pour la Tribu des enfants de Zabulon, celui qui en est le chef, Elitsaphan, fils de Parnac.
26 Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
Pour la Tribu des enfants d'Issacar, celui qui en est le chef, Paltiel, fils de Hazan.
27 Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
Pour la Tribu des enfants d'Aser, celui qui en est le chef, Ahihud, fils de Sélomi.
28 Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
Et pour la Tribu des enfants de Nephthali, celui qui en est le chef, Pédahel, fils de Hammiud.
29 Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.
Ce sont là ceux auxquels l'Eternel commanda de partager l'héritage aux enfants d'Israël dans le pays de Canaan.

< Ƙidaya 34 >