< Ƙidaya 34 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
2 “Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
“Command the sons of Israel, and you have said to them: When you are coming into the land of Canaan—this [is] the land which falls to you by inheritance, the land of Canaan, by its borders—
3 “‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
then the south quarter has been to you from the wilderness of Zin, by the sides of Edom, indeed, the south border has been to you from the extremity of the Salt Sea eastward;
4 tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
and the border has turned around to you from the south to the ascent of Akrabbim, and has passed on to Zin, and its outgoings have been from the south to Kadesh-Barnea, and it has gone out at Hazar-Addar, and has passed on to Azmon;
5 inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
and the border has turned around from Azmon to the Brook of Egypt, and its outgoings have been at the sea.
6 “‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
As for the west border, even the Great Sea has been a border to you; this is the west border to you.
7 “‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
And this is the north border to you: from the Great Sea you mark out for yourselves Mount Hor;
8 za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
from Mount Hor you mark out to go to Hamath, and the outgoings of the border have been to Zedad;
9 tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
and the border has gone out to Ziphron, and its outgoings have been at Hazar-Enan; this is the north border to you.
10 “‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
And you have marked out for yourselves for the border eastward, from Hazar-Enan to Shepham;
11 Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
and the border has gone down from Shepham to Riblah, on the east of Ain, and the border has gone down, and has struck against the shoulder of the Sea of Chinnereth eastward;
12 Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
and the border has gone down to the Jordan, and its outgoings have been at the Salt Sea; this is the land for you by its borders all around.”
13 Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
And Moses commands the sons of Israel, saying, “This [is] the land which you inherit by lot, which YHWH has commanded to give to the nine tribes and the half of the tribe;
14 saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
for the tribe of the sons of Reuben, by the house of their fathers, and the tribe of the children of Gad, by the house of their fathers, have received [their inheritance]; and [those of] the half of the tribe of Manasseh have received their inheritance;
15 Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
the two tribes and the half of the tribe have received their inheritance beyond the Jordan, [near] Jericho, eastward, at the [sun]-rising.”
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
17 “Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
“These [are] the names of the men who give the inheritance of the land to you: Eleazar the priest and Joshua son of Nun.
18 Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
And one prince—you take one prince from a tribe to give the land by inheritance.
19 “Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
And these [are] the names of the men: of the tribe of Judah, Caleb son of Jephunneh;
20 Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
and of the tribe of the sons of Simeon, Shemuel son of Aminihud;
21 Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
of the tribe of Benjamin, Elidad son of Chislon;
22 Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
and a prince of the tribe of the sons of Dan, Bukki son of Jogli;
23 Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
of the sons of Joseph, a prince of the tribe of the sons of Manasseh, Hanniel son of Ephod;
24 Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
and a prince of the tribe of the sons of Ephraim, Kemuel son of Shiphtan;
25 Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
and a prince of the tribe of the sons of Zebulun, Elizaphan son of Parnach;
26 Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
and a prince of the tribe of the sons of Issachar, Paltiel son of Azzan;
27 Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
and a prince of the tribe of the sons of Asher, Ahihud son of Shelomi;
28 Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
and a prince of the tribe of the sons of Naphtali, Pedahel son of Ammihud.”
29 Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.
These [are] those whom YHWH has commanded to give the sons of Israel inheritance in the land of Canaan.

< Ƙidaya 34 >