< Ƙidaya 34 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke unto Moses, saying:
2 “Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
'Command the children of Israel, and say unto them: When ye come into the land of Canaan, this shall be the land that shall fall unto you for an inheritance, even the land of Canaan according to the borders thereof.
3 “‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
Thus your south side shall be from the wilderness of Zin close by the side of Edom, and your south border shall begin at the end of the Salt Sea eastward;
4 tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
and your border shall turn about southward of the ascent of Akrabbim, and pass along to Zin; and the goings out thereof shall be southward of Kadesh-barnea; and it shall go forth to Hazar-addar, and pass along to Azmon;
5 inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
and the border shall turn about from Azmon unto the Brook of Egypt, and the goings out thereof shall be at the Sea.
6 “‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
And for the western border, ye shall have the Great Sea for a border; this shall be your west border.
7 “‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
And this shall be your north border: from the Great Sea ye shall mark out your line unto mount Hor;
8 za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
from mount Hor ye shall mark out a line unto the entrance to Hamath; and the goings out of the border shall be at Zedad;
9 tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
and the border shall go forth to Ziphron, and the goings out thereof shall be at Hazar-enan; this shall be your north border.
10 “‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
And ye shall mark out your line for the east border from Hazar-enan to Shepham;
11 Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
and the border shall go down from Shepham to Riblah, on the east side of Ain; and the border shall go down, and shall strike upon the slope of the sea of Chinnereth eastward;
12 Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
and the border shall go down to the Jordan, and the goings out thereof shall be at the Salt Sea; this shall be your land according to the borders thereof round about.'
13 Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
And Moses commanded the children of Israel, saying: 'This is the land wherein ye shall receive inheritance by lot, which the LORD hath commanded to give unto the nine tribes, and to the half-tribe;
14 saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
for the tribe of the children of Reuben according to their fathers' houses, and the tribe of the children of Gad according to their fathers' houses, have received, and the half-tribe of Manasseh have received, their inheritance;
15 Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
the two tribes and the half-tribe have received their inheritance beyond the Jordan at Jericho eastward, toward the sun-rising.'
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke unto Moses, saying:
17 “Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
'These are the names of the men that shall take possession of the land for you: Eleazar the priest, and Joshua the son of Nun.
18 Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
And ye shall take one prince of every tribe, to take possession of the land.
19 “Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
And these are the names of the men: of the tribe of Judah, Caleb the son of Jephunneh.
20 Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
And of the tribe of the children of Simeon, Shemuel the son of Ammihud.
21 Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
Of the tribe of Benjamin, Elidad the son of Chislon.
22 Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
And of the tribe of the children of Dan a prince, Bukki the son of Jogli.
23 Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
Of the children of Joseph: of the tribe of the children of Manasseh a prince, Hanniel the son of Ephod;
24 Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
and of the tribe of the children of Ephraim a prince, Kemuel the son of Shiphtan.
25 Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
And of the tribe of the children of Zebulun a prince, Eli-zaphan the son of Parnach.
26 Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
And of the tribe of the children of Issachar a prince, Paltiel the son of Azzan.
27 Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
And of the tribe of the children of Asher a prince, Ahihud the son of Shelomi.
28 Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
And of the tribe of the children of Naphtali a prince, Pedahel the son of Ammihud.
29 Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.
These are they whom the LORD commanded to divide the inheritance unto the children of Israel in the land of Canaan.'