< Ƙidaya 33 >
1 Ga wuraren da Isra’ilawa suka yi sansani sa’ad da suka fito runduna-runduna a ƙarƙashin Musa da Haruna daga Masar.
Nanka amalombolombo ohambo lwabako-Israyeli ekuphumeni kwabo eGibhithe ngamaviyo abo bekhokhelwa nguMosi lo-Aroni.
2 Bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya rubuta wuraren tafiye-tafiyensu da sansaninsu. Ga yadda tafiye-tafiyen suka kasance.
Ngokulaya kukaThixo waloba walonda izigaba zamalombolombo ohambo lwabo. Nantu uhambo lwabo ngezigaba zakhona:
3 Isra’ilawa sun tashi daga Rameses a rana ta goma sha biyar, ga watan fari, kashegarin Bikin Ƙetarewa. Suka fita gabagadi a gaban dukan Masarawa,
Abako-Israyeli basuka eRamesesi ngosuku lwetshumi lanhlanu lwenyanga yakuqala, ngosuku kwedlule iPhasika. Baphuma ngesibindi bekhangelwe ngamaGibhithe wonke,
4 waɗanda suke binne gawawwakin’ya’yan farinsu da Ubangiji ya karkashe; gama Ubangiji ya hukunta allolinsu.
wona eyephathekile engcwaba wonke amazibulo awo, lawo ayebulewe nguThixo phakathi kwawo; ngoba uThixo wayehlulele ngokujezisa onkulunkulu bawo.
5 Isra’ilawa suka tashi daga Rameses, suka yi sansani a Sukkot.
Abako-Israyeli basuka eRamesesi bayamisa izihonqo zabo eSukhothi.
6 Suka tashi daga Sukkot, suka yi sansani a Etam, a gefen hamada.
Basuka eSukhothi bayamisa izihonqo zabo e-Ethamu, emaphethelweni enkangala.
7 Suka tashi daga Etam, suka koma baya zuwa Fi Hahirot, wajen gabashin Ba’al-Zafon, suka yi sansani kusa da Migdol.
Basuka e-Ethamu, baphenduka baya ePhi-Hahirothi; beqonda empumalanga yaseBhali-Zefoni, babuye njalo bamisa izihonqo zabo eMigidoli.
8 Suka tashi daga Fi Hahirot, suka ratsa cikin teku zuwa hamada, bayan sun yi tafiya kwana uku a cikin Hamadan Etam, sai suka yi sansani a Mara.
Basuka ePhi-Hahirothi badabula olwandle bangena enkangala, bathi sebehambe okwensuku ezintathu enkangala ye-Ethamu, bamisa izihonqo zabo eMara.
9 Suka tashi daga Mara, suka tafi Elim, inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu, da itatuwan dabino guda saba’in, suka yi sansani a can.
Basuka eMara baya e-Elimi, lapho okwakulezintombo zamanzi ezilitshumi lambili kanye lezihlahla zohlobo lwelala ezingamatshumi ayisikhombisa, bafika bamisa izihonqo khonapho.
10 Suka tashi daga Elim, suka yi sansani kusa da Jan Teku.
Basuka e-Elimi bayamisa izihonqo zabo besekele uLwandle oluBomvu.
11 Suka tashi daga Jan Teku, suka yi sansani a Hamadan Sin.
Basuka oLwandle oluBomvu bayamisa enkangala yaseSini.
12 Suka tashi daga Hamadan Sin, suka yi sansani a Dofka.
Basuka enkangala yeSini bayamisa eDofuka.
13 Suka tashi daga Dofka, suka yi sansani a Alush.
Basuka eDofuka bayamisa e-Alusha.
14 Suka tashi daga Alush, suka yi sansani a Refidim, inda babu ruwan da mutane za su sha.
Basuka e-Alusha bayamisa eRefidimu, lapho okwakungelamanzi okunathwa ngabantu.
15 Suka tashi daga Refidim, suka yi sansani a Hamadan Sinai.
Basuka eRefidimu bayamisa enkangala yeSinayi.
16 Suka tashi daga Hamadan Sinai, suka yi sansani a Kibrot Hatta’awa.
Basuka enkangala yeSinayi bayamisa eKhibhrothi Hathava.
17 Suka tashi daga Kibrot Hatta’awa, suka yi sansani a Hazerot.
Basuka eKhibhrothi Hathava bayamisa eHazerothi.
18 Suka tashi daga Hazerot, suka yi sansani a Ritma.
Basuka eHazerothi bayamisa eRithima.
19 Suka tashi daga Ritma, suka yi sansani a Rimmon Ferez.
Basuka eRithima bayamisa eRimoni-Pherezi.
20 Suka tashi daga Rimmon Ferez, suka yi sansani a Libna.
Basuka eRimoni-Pherezi bayamisa eLibhina.
21 Suka tashi daga Libna, suka yi sansani a Rissa.
Basuka eLibhina bayamisa eRisa.
22 Suka tashi daga Rissa, suka yi sansani a Kehelata.
Basuka eRisa bayamisa eKhehelatha.
23 Suka tashi daga Kehelata, suka yi sansani a Dutsen Shefer.
Basuka eKhehelatha bayamisa eNtabeni yaseShefa.
24 Suka tashi daga Dutsen Shefer, suka yi sansani a Harada.
Basuka eNtabeni yaseShefa bayamisa eHarada.
25 Suka tashi daga Harada, suka yi sansani a Makhelot.
Basuka eHarada bayamisa eMakhelothi.
26 Suka tashi daga Makhelot, suka yi sansani a Tahat.
Basuka eMakhelothi bayamisa eThahathi.
27 Suka tashi daga Tahat, suka yi sansani a Tera.
Basuka eThahathi bayamisa eThera.
28 Suka tashi daga Tera, suka yi sansani a Mitka.
Basuka eThera bayamisa eMithika.
29 Suka tashi daga Mitka, suka yi sansani a Hashmona.
Basuka eMithika bayamisa eHashimona.
30 Suka tashi daga Hashmona, suka yi sansani a Moserot.
Basuka eHashimona bayamisa eMosera.
31 Suka tashi daga Moserot, suka yi sansani a Bene Ya’akan.
Basuka eMosera bayamisa eBhene Jayakhani.
32 Suka tashi daga Bene Ya’akan, suka yi sansani a Hor Haggidgad.
Basuka eBhene Jayakhani bayamisa eHori-Hagidigadi.
33 Suka tashi daga Hor Haggidgad, suka yi sansani a Yotbata.
Basuka eHori-Hagidigadi bayamisa eJothibhatha.
34 Suka tashi daga Yotbata, suka yi sansani a Abrona.
Basuka eJothibhatha bayamisa e-Abhurona.
35 Suka tashi daga Abrona, suka yi sansani a Eziyon Geber.
Basuka e-Abhurona bayamisa e-Eziyoni-Gebheri.
36 Suka tashi daga Eziyon Geber, suka yi sansani a Kadesh, cikin Hamadan Zin.
Basuka e-Eziyoni-Gebheri bayamisa eKhadeshi, eNkangala yaseZini.
37 Suka tashi daga Kadesh, suka yi sansani a Dutsen Hor, a iyakar Edom.
Basuka eKhadeshi bayamisa eNtabeni yaseHori, emngceleni wase-Edomi.
38 Bisa ga umarni Ubangiji, Haruna firist, ya hau Dutsen Hor, inda ya mutu a rana ta fari ga watan biyar, a shekara ta arba’in, bayan Isra’ilawa suka fito daga Masar.
Ngokulaya kukaThixo, u-Aroni umphristi wakhwela eNtabeni yaseHori, lapho afela khona ngosuku lwakuqala lwenyanga yesihlanu yomnyaka wamatshumi amane emva kokuphuma kwabako-Israyeli eGibhithe.
39 Haruna yana da shekara ɗari da ashirin da uku, sa’ad da ya mutu a Dutsen Hor.
U-Aroni wayeseleminyaka elikhulu elileminyaka engamatshumi amabili lemithathu yokuphila ekufeni kwakhe eNtabeni yaseHori.
40 Sarki Arad Bakan’ane, wanda yake zaune a Negeb na Kan’ana, ya ji labari cewa Isra’ilawa suna zuwa.
Inkosi yase-Aradi engumKhenani eyayihlala eNegebi yaseKhenani, yezwa ukuthi abako-Israyeli babesiza.
41 Suka tashi daga Dutsen Hor, suka yi sansani a Zalmona.
Basuka eNtabeni yaseHori bayamisa eZalimona.
42 Suka tashi daga Zalmona, suka yi sansani a Funon.
Basuka eZalimona bayamisa ePhunoni.
43 Suka tashi daga Funon, suka yi sansani a Obot.
Basuka ePhunoni bayamisa e-Obhothi.
44 Suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim, a iyakar Mowab.
Basuka e-Obhothi bayamisa e-Iye-Abharimi, emngceleni waseMowabi.
45 Suka tashi daga Iyim, suka yi sansani a Dibon Gad.
Basuka e-Iye-Abharimu bayamisa eDibhoni Gadi.
46 Suka tashi daga Dibon Gad, suka yi sansani a Almon Dibilatayim.
Basuka eDibhoni Gadi bayamisa e-Alimoni-Dibhilathayimi.
47 Suka tashi daga Almon Dibilatayim, suka yi sansani a duwatsun Abarim, kusa da Nebo.
Basuka e-Alimoni-Dibhilathayimi bayamisa ezintabeni zase-Abharimi, phansi kweNebho.
48 Suka tashi daga duwatsun Abarim, suka yi sansani a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
Basuka ezintabeni zase-Abharimi bayamisa emagcekeni aseMowabi besekele uJodani ngaphetsheya malungana leJerikho.
49 A can filayen Mowab, suka yi sansani kusa da Urdun ɗaura da Bet-Yeshimot har zuwa Abel-Shittim.
Khonapho emagcekeni aseMowabi bamisa izihonqo zabo belandela umfula uJodani kusukela eBhethi-Jeshimothi kusiya e-Abheli-Shithima.
50 A filayen Mowab kusa da Urdun ɗaura da Yeriko ne Ubangiji ya ce wa Musa,
Emagcekeni aseMowabi ngasemfuleni uJodani ngaphetsheya uvelela ngaseJerikho uThixo wathi kuMosi,
51 “Ka gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
“Khuluma kwabako-Israyeli ubatshele lokhu uthi: ‘Nxa lichapha uJodani lingena eKhenani,
52 ku kori dukan mazaunan ƙasar a gabanku. Ku rurrushe sassaƙaƙƙun duwatsu, da siffofinsu na zubi, ku kuma rurrushe dukan masujadansu na kan tudu.
xotshani phambi kwenu bonke abahlala kulelolizwe. Dilizani zonke izithombe zabo ezibaziweyo kanye lezibunjiweyo, njalo libhidlize zonke izindawo eziphakemeyo zokukhonzela.
53 Ku mallaki ƙasar, ku kuma zauna a ciki, gama na ba ku ƙasar, ku mallake ta.
Thumbani ilizwe lelo lihlale kulo, ngoba ngilinike ukuthi libe ngelenu.
54 Ku rarraba ƙasar ta wurin jefan ƙuri’a, bisa ga kabilanku. Kabilar da take babba, a ba ta babban gādo, ƙarami kabila kuwa, a ba ta ƙaramin gādo. Duk abin da ƙuri’a ta ba su, shi zai zama nasu. Ku rarraba wannan bisa zuriyar kakanninku.
Yabelanani ilizwe ngenkatho, kusiya ngokwensendo zenu. Ixuku elikhulu kaliphiwe isabelo esikhulu, kuthi ixuku elincinyane liphiwe isabelo esincinyane. Okuzakuya kubo ngenkatho akube ngokwabo. Kwabelananeni kusiya ngezizwana zabokhokho benu.
55 “‘Amma in ba ku kori mazaunan ƙasar ba, waɗanda kuka bari su ci gaba da zama, za su zama muku hakki a idanunku, da kuma ƙayayyuwa a bayanku. Za su ba ku wahala a ƙasar da kuke zama.
Kodwa nxa lingaxotshanga abahlala kulelolizwe, abaseleyo babo bazakuba lukhophe emehlweni enu njalo babe ngameva enyameni yenu. Bazakuba luhlupho ezweni elizahlala kulo.
56 Sa’an nan kuwa zan yi muku abin da na shirya yin musu.’”
Ngakho-ke ngizakwenza kini lokho engizimisele ukukwenza kubo.’”