< Ƙidaya 32 >

1 Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
A sinovi Ruvimovi i sinovi Gadovi imahu vrlo mnogo stoke, i vidješe zemlju Jazirsku i zemlju Galadsku da je dobra za stoku.
2 Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
I došavši sinovi Gadovi i sinovi Ruvimovi rekoše Mojsiju i Eleazaru svešteniku i knezovima od zbora govoreæi:
3 “Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
Atarot i Devon i Jazir i Namra i Esevon i Elealija i Sevama i Navav i Vean,
4 ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
Ta je zemlja, koju Gospod pokori zboru Izrailjskom, dobra za stoku, a sluge tvoje imaju stoke.
5 Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
Ako smo, rekoše, našli milost pred tobom, neka se ta zemlja dade slugama tvojim u našljedstvo, nemoj nas voditi preko Jordana.
6 Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
A Mojsije reèe sinovima Gadovijem i sinovima Ruvimovijem: braæa æe vaša iæi na vojsku, a vi hoæete ovdje da ostanete?
7 Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
Zašto obarate srce sinovima Izrailjevijem da ne prijeðu u zemlju koju im je dao Gospod?
8 Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
Tako su uèinili oci vaši, kad ih poslah iz Kadis-Varne da uhode zemlju;
9 Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
I otidoše do potoka Eshola, i uhodiše zemlju; i oboriše srce sinovima Izrailjevijem da ne idu u zemlju koju im dade Gospod;
10 A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
I razgnjevi se onda Gospod, i zakle se govoreæi:
11 ‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
Neæe ti ljudi koji izaðoše iz Misira, od dvadeset godina i više, vidjeti zemlje za koju se zakleh Avramu, Isaku i Jakovu, jer se ne držaše mene sasvijem,
12 ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
Osim Haleva sina Jefonijina Kenezeja i Isusa sina Navina, jer se sasvijem držaše Gospoda.
13 Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
I razgnjevi se Gospod na Izrailja, i uèini te se potucaše po pustinji èetrdeset godina, dokle ne pomrije sav onaj naraštaj koji èinjaše zlo pred Gospodom.
14 “Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
A vi sada izaðoste na mjesto otaca svojih, rod griješnih ljudi, da umnožavate žestinu gnjeva Gospodnjega na Izrailja.
15 In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
Ako se odvratite od njega, on æe ga još ostaviti u pustinji, i tako æete upropastiti sav onaj narod.
16 Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
A oni pristupiše opet k njemu, i rekoše mu: mi smo radi samo torove naèiniti ovdje za stada svoja i gradove za djecu svoju.
17 Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
A sami æemo naoružani junaèki poæi pred sinovima Izrailjevijem, dokle ih ne odvedemo na njihovo mjesto; a naša djeca neka stoje u gradovima tvrdijem radi stanovnika te zemlje.
18 Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
Neæemo se vratiti kuæama svojim dokle sinovi Izrailjevi ne prime svaki svoje našljedstvo.
19 Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
Niti æemo uzeti našljedstva s njima s onu stranu Jordana ni dalje, ako nam dopadne našljedstvo s ovu stranu Jordana prema istoku.
20 Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
Tada im reèe Mojsije: ako æete uèiniti tako i iæi pod oružjem pred Gospodom na vojsku,
21 in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
Ako svaki od vas pod oružjem prijeðe preko Jordana pred Gospodom, dokle ne otjera ispred sebe neprijatelja svojih,
22 to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
I dokle se ne pokori zemlja pred Gospodom, pa se onda vratite i ne zgriješite Gospodu ni Izrailju, onda æe ova zemlja pripasti vama u našljedstvo pred Gospodom.
23 “Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
Ako li ne uèinite tako, gle, zgriješiæete Gospodu, i znajte da æe vas grijeh vaš stiæi.
24 Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
Gradite sebi gradove za djecu svoju i torove za stoku svoju; i što je izašlo iz usta vaših, uèinite.
25 Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
I rekoše Mojsiju sinovi Gadovi i sinovi Ruvimovi govoreæi: sluge æe tvoje uèiniti kako gospodar naš zapovijeda.
26 ’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
Djeca naša i žene naše, stada naša i sva stoka naša ovdje æe ostati u gradovima Galadskim;
27 Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
A sluge æe tvoje prijeæi svaki naoružan, da se bije pred Gospodom, kao što govori gospodar naš.
28 Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
Tada Mojsije zapovjedi za njih Eleazaru svešteniku i Isusu sinu Navinu i glavarima od domova otaèkih meðu sinovima Izrailjevijem,
29 ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
I reèe im: ako prijeðu sinovi Gadovi i sinovi Ruvimovi s vama preko Jordana, svi oružani, da se biju pred Gospodom, i kad vam bude zemlja pokorena, onda podajte njima zemlju Galadsku u našljedstvo.
30 Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
Ako li ne prijeðu s vama pod oružjem, onda neka im bude našljedstvo meðu vama u zemlji Hananskoj.
31 Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
I odgovoriše sinovi Gadovi i sinovi Ruvimovi govoreæi: kako je Gospod kazao slugama tvojim tako æemo uèiniti.
32 Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
Prijeæi æemo pod oružjem pred Gospodom u zemlju Hanansku, a naše našljedstvo da bude s ovu stranu Jordana.
33 Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
I dade Mojsije sinovima Gadovijem i sinovima Ruvimovijem i polovini plemena Manasije sina Josifova carstvo Siona cara Amorejskoga i carstvo Oga cara Vasanskoga, zemlju i gradove po meðama njezinijem, gradove one zemlje unaokolo.
34 Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
I sagradiše sinovi Gadovi Devon i Atarot i Aroir.
35 Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
I Atrot-Sofan i Jazir i Jogveju,
36 Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
I Vet-Nimru i Vet-Aran, gradove tvrde, i torove za stoku.
37 Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
A sinovi Ruvimovi sagradiše Esevon i Elealiju i Kirijatajim,
38 haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
I Navon i Velmeon predjenuvši im imena, i Sivmu; i nadješe druga imena gradovima koje sagradiše.
39 Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
A sinovi Mahira sina Manasijina otidoše u Galad, i uzeše ga, i izagnaše Amoreje koji bijahu ondje.
40 Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
I Mojsije dade Galad Mahiru sinu Manasijinu, koji se ondje naseli.
41 Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
I Jair sin Manasijin otide i uze sela njihova i prozva ih sela Jairova.
42 Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.
I Navav otide i uze Kenat sa selima njegovijem, i prozva ga Navav po imenu svojemu.

< Ƙidaya 32 >