< Ƙidaya 32 >
1 Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
Et les troupeaux des fils de Ruben et des fils de Gad étaient en grand nombre, en très grande quantité. Et ils virent le pays de Jahzer et le pays de Galaad, et voici, le lieu était un lieu propre pour des troupeaux.
2 Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
Et les fils de Gad et les fils de Ruben vinrent, et parlèrent à Moïse et à Éléazar, le sacrificateur, et aux princes de l’assemblée, disant:
3 “Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
Ataroth, et Dibon, et Jahzer, et Nimra, et Hesbon, et Elhalé, et Sebam, et Nebo, et Béon,
4 ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
le pays que l’Éternel a frappé devant l’assemblée d’Israël, est un pays propre pour des troupeaux, et tes serviteurs ont des troupeaux.
5 Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
Et ils dirent: Si nous avons trouvé faveur à tes yeux, que ce pays soit donné en possession à tes serviteurs; ne nous fais pas passer le Jourdain.
6 Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
Et Moïse dit aux fils de Gad et aux fils de Ruben: Vos frères iront-ils à la guerre, et vous, vous habiterez ici?
7 Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
Et pourquoi découragez-vous les fils d’Israël de passer dans le pays que l’Éternel leur a donné?
8 Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
Ainsi firent vos pères lorsque je les envoyai de Kadès-Barnéa pour voir le pays:
9 Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
ils montèrent à la vallée d’Eshcol, et virent le pays; et ils découragèrent les fils d’Israël, afin qu’ils n’entrent pas dans le pays que l’Éternel leur avait donné.
10 A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
Et la colère de l’Éternel s’embrasa en ce jour-là, et il jura, disant:
11 ‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
Si les hommes qui sont montés d’Égypte, depuis l’âge de 20 ans et au-dessus, voient la terre que j’ai promise par serment à Abraham, à Isaac, et à Jacob! car ils ne m’ont pas pleinement suivi,
12 ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
– excepté Caleb, fils de Jephunné, le Kenizien, et Josué, fils de Nun, car ils ont pleinement suivi l’Éternel.
13 Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
Et la colère de l’Éternel s’embrasa contre Israël, et il les a fait errer dans le désert 40 ans, jusqu’à ce qu’ait péri toute la génération qui avait fait ce qui est mauvais aux yeux de l’Éternel.
14 “Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
Et voici, vous vous êtes levés à la place de vos pères, une progéniture d’hommes pécheurs, pour ajouter encore à l’ardeur de la colère de l’Éternel contre Israël.
15 In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
Si vous vous détournez de lui, il le laissera encore dans le désert, et vous détruirez tout ce peuple.
16 Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
Et ils s’approchèrent de lui, et dirent: Nous bâtirons ici des enclos pour nos troupeaux, et des villes pour nos petits enfants;
17 Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
et nous nous équiperons promptement [pour marcher] devant les fils d’Israël, jusqu’à ce que nous les ayons introduits en leur lieu; et nos petits enfants habiteront dans les villes fortes, à cause des habitants du pays.
18 Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
Nous ne reviendrons pas dans nos maisons, jusqu’à ce que les fils d’Israël aient pris possession chacun de son héritage;
19 Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
car nous n’hériterons pas avec eux au-delà du Jourdain, ni plus loin, parce que notre héritage nous est échu, à nous, de ce côté du Jourdain, vers le levant.
20 Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
Et Moïse leur dit: Si vous faites cela, si vous vous équipez devant l’Éternel pour la guerre,
21 in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
et que tous ceux d’entre vous qui sont équipés passent le Jourdain devant l’Éternel, jusqu’à ce qu’il ait dépossédé ses ennemis devant lui,
22 to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
et que le pays soit subjugué devant l’Éternel, et qu’ensuite vous vous en retourniez, alors vous serez innocents envers l’Éternel et envers Israël; et ce pays-ci sera votre possession devant l’Éternel.
23 “Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
Mais si vous ne faites pas ainsi, voici, vous pécherez contre l’Éternel; et sachez que votre péché vous trouvera.
24 Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
Bâtissez-vous des villes pour vos petits enfants, et des enclos pour vos troupeaux; et ce qui est sorti de votre bouche, faites-le.
25 Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
Et les fils de Gad et les fils de Ruben parlèrent à Moïse, disant: Tes serviteurs feront comme mon seigneur l’a commandé.
26 ’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
Nos petits enfants, nos femmes, nos troupeaux et toutes nos bêtes seront là, dans les villes de Galaad;
27 Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
et tes serviteurs, tous équipés pour l’armée, passeront devant l’Éternel [pour aller] à la guerre, comme mon seigneur l’a dit.
28 Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
Et Moïse commanda à leur sujet à Éléazar, le sacrificateur, et à Josué, fils de Nun, et aux chefs des pères des tribus des fils d’Israël;
29 ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
et Moïse leur dit: Si les fils de Gad et les fils de Ruben passent avec vous le Jourdain devant l’Éternel, tous équipés pour la guerre, et que le pays soit subjugué devant vous, vous leur donnerez le pays de Galaad en possession.
30 Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
Mais s’ils ne passent pas équipés avec vous, alors ils auront des possessions au milieu de vous dans le pays de Canaan.
31 Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
Et les fils de Gad et les fils de Ruben répondirent, disant: Nous ferons ainsi que l’Éternel a dit à tes serviteurs;
32 Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
nous passerons équipés devant l’Éternel dans le pays de Canaan, et la possession de notre héritage en deçà du Jourdain sera à nous.
33 Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
Et Moïse leur donna, – aux fils de Gad, et aux fils de Ruben, et à la demi-tribu de Manassé, fils de Joseph, – le royaume de Sihon, roi des Amoréens, et le royaume d’Og, roi de Basan, le pays, selon ses villes, dans leurs confins, les villes du pays à l’entour.
34 Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
– Et les fils de Gad bâtirent Dibon, et Ataroth, et Aroër,
35 Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
et Atroth-Shophan, et Jahzer, et Jogbeha,
36 Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
et Beth-Nimra, et Beth-Haran, villes fortes, et des enclos pour le petit bétail.
37 Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
– Et les fils de Ruben bâtirent Hesbon, et Elhalé, et Kiriathaïm,
38 haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
et Nebo, et Baal-Méon, dont les noms furent changés, et Sibma; et ils donnèrent d’autres noms aux villes qu’ils bâtirent.
39 Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
– Et les fils de Makir, fils de Manassé, allèrent dans [le pays de] Galaad, et le prirent, et dépossédèrent les Amoréens qui y étaient.
40 Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
Et Moïse donna Galaad à Makir, fils de Manassé, et il y habita.
41 Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
Et Jaïr, fils de Manassé, alla, et prit leurs bourgs, et les appela bourgs de Jaïr.
42 Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.
Et Nobakh alla, et prit Kenath et les villages de son ressort, et il l’appela Nobakh, d’après son nom.