< Ƙidaya 32 >

1 Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
and livestock many to be to/for son: descendant/people Reuben and to/for son: descendant/people Gad mighty much and to see: see [obj] land: country/planet Jazer and [obj] land: country/planet Gilead and behold [the] place place livestock
2 Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
and to come (in): come son: descendant/people Gad and son: descendant/people Reuben and to say to(wards) Moses and to(wards) Eleazar [the] priest and to(wards) leader [the] congregation to/for to say
3 “Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
Ataroth and Dibon and Jazer and Nimrah and Heshbon and Elealeh and Sebam and Nebo and Beon
4 ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
[the] land: country/planet which to smite LORD to/for face: before congregation Israel land: country/planet livestock he/she/it and to/for servant/slave your livestock
5 Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
and to say if to find favor in/on/with eye: seeing your to give: give [obj] [the] land: country/planet [the] this to/for servant/slave your to/for possession not to pass us [obj] [the] Jordan
6 Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
and to say Moses to/for son: descendant/people Gad and to/for son: descendant/people Reuben brother: compatriot your to come (in): come to/for battle and you(m. p.) to dwell here
7 Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
and to/for what? (to forbid [emph?] *Q(K)*) [obj] heart son: descendant/people Israel from to pass to(wards) [the] land: country/planet which to give: give to/for them LORD
8 Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
thus to make: do father your in/on/with to send: depart I [obj] them from Kadesh-barnea Kadesh-barnea to/for to see: see [obj] [the] land: country/planet
9 Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
and to ascend: rise till (Eshcol) Valley (Valley of) Eshcol and to see: see [obj] [the] land: country/planet and to forbid [obj] heart son: descendant/people Israel to/for lest to come (in): come to(wards) [the] land: country/planet which to give: give to/for them LORD
10 A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
and to be incensed face: anger LORD in/on/with day [the] he/she/it and to swear to/for to say
11 ‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
if to see: see [the] human [the] to ascend: rise from Egypt from son: aged twenty year and above [to] [obj] [the] land: soil which to swear to/for Abraham to/for Isaac and to/for Jacob for not to fill after me
12 ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
lest Caleb son: child Jephunneh [the] Kenizzite and Joshua son: child Nun for to fill after LORD
13 Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
and to be incensed face: anger LORD in/on/with Israel and to shake them in/on/with wilderness forty year till to finish all [the] generation [the] to make: do [the] bad: evil in/on/with eye: seeing LORD
14 “Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
and behold to arise: rise underneath: instead father your increase human sinner to/for to snatch still upon burning anger face: anger LORD to(wards) Israel
15 In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
for to return: turn back [emph?] from after him and to add: again still to/for to rest him in/on/with wilderness and to ruin to/for all [the] people [the] this
16 Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
and to approach: approach to(wards) him and to say wall flock to build to/for livestock our here and city to/for child our
17 Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
and we to arm to hasten to/for face: before son: descendant/people Israel till which if: until to come (in): bring them to(wards) place their and to dwell child our in/on/with city [the] fortification from face: because to dwell [the] land: country/planet
18 Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
not to return: return to(wards) house: home our till to inherit son: descendant/people Israel man: anyone inheritance his
19 Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
for not to inherit with them from side: beside to/for Jordan and further for to come (in): come inheritance our to(wards) us from side: beside [the] Jordan east [to]
20 Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
and to say to(wards) them Moses if to make: do [emph?] [obj] [the] word: thing [the] this if to arm to/for face: before LORD to/for battle
21 in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
and to pass to/for you all to arm [obj] [the] Jordan to/for face: before LORD till to possess: take he [obj] enemy his from face: before his
22 to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
and to subdue [the] land: country/planet to/for face: before LORD and after to return: return and to be innocent from LORD and from Israel and to be [the] land: country/planet [the] this to/for you to/for possession to/for face: before LORD
23 “Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
and if not to make: do [emph?] so behold to sin to/for LORD and to know sin your which to find [obj] you
24 Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
to build to/for you city to/for child your and wall to/for sheep your and [the] to come out: speak from lip your to make: do
25 Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
and to say son: descendant/people Gad and son: descendant/people Reuben to(wards) Moses to/for to say servant/slave your to make: do like/as as which lord my to command
26 ’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
child our woman: wife our livestock our and all animal our to be there in/on/with city [the] Gilead
27 Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
and servant/slave your to pass all to arm army: war to/for face: before LORD to/for battle like/as as which lord my to speak: speak
28 Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
and to command to/for them Moses [obj] Eleazar [the] priest and [obj] Joshua son: child Nun and [obj] head: leader father [the] tribe to/for son: descendant/people Israel
29 ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
and to say Moses to(wards) them if to pass son: descendant/people Gad and son: descendant/people Reuben with you [obj] [the] Jordan all to arm to/for battle to/for face: before LORD and to subdue [the] land: country/planet to/for face: before your and to give: give to/for them [obj] land: country/planet [the] Gilead to/for possession
30 Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
and if not to pass to arm with you and to grasp in/on/with midst your in/on/with land: country/planet Canaan
31 Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
and to answer son: descendant/people Gad and son: descendant/people Reuben to/for to say [obj] which to speak: speak LORD to(wards) servant/slave your so to make: do
32 Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
we to pass to arm to/for face: before LORD land: country/planet Canaan and with us possession inheritance our from side: beyond to/for Jordan
33 Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
and to give: give to/for them Moses to/for son: descendant/people Gad and to/for son: descendant/people Reuben and to/for half tribe Manasseh son: child Joseph [obj] kingdom Sihon king [the] Amorite and [obj] kingdom Og king [the] Bashan [the] land: country/planet to/for city her in/on/with border city [the] land: country/planet around: whole
34 Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
and to build son: descendant/people Gad [obj] Dibon and [obj] Ataroth and [obj] Aroer
35 Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
and [obj] Atroth-shophan Atroth-shophan and [obj] Jazer and Jogbehah
36 Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
and [obj] Beth-nimrah Beth-nimrah and [obj] Beth-haran Beth-haran city fortification and wall flock
37 Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
and son: descendant/people Reuben to build [obj] Heshbon and [obj] Elealeh and [obj] Kiriathaim
38 haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
and [obj] Nebo and [obj] Baal-meon Baal-meon to turn: turn name and [obj] Sibmah and to call: call by in/on/with name [obj] name [the] city which to build
39 Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
and to go: went son: descendant/people Machir son: child Manasseh Gilead [to] and to capture her and to possess: take [obj] [the] Amorite which in/on/with her
40 Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
and to give: give Moses [obj] [the] Gilead to/for Machir son: child Manasseh and to dwell in/on/with her
41 Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
and Jair son: descendant/people Manasseh to go: went and to capture [obj] village their and to call: call by [obj] them Havvoth-jair Havvoth-jair
42 Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.
and Nobah to go: went and to capture [obj] Kenath and [obj] daughter: village her and to call: call by to/for her Nobah in/on/with name his

< Ƙidaya 32 >