< Ƙidaya 32 >

1 Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
Rubeniterne og Gaditerne havde meget Kvæg i store mængder. Da de nu saa Ja'zers Land og Gileads Land, fandt de, at Stedet egnede sig til Kvægavl.
2 Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
Derfor kom Gaditerne og Rubeniterne og sagde til Moses og Præsten Eleazar og Menighedens Øverste:
3 “Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
»Atarot, Dibon, Ja'zer, Nimra, Hesjbon, El'ale, Sebam, Nebo og Beon,
4 ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
det Land, HERREN har erobret for Israels Menighed, er et Land, der egner sig til Kvægavl, og dine Trælle ejer Hjorde.«
5 Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
Og de sagde: »Dersom vi har fundet Naade for dine Øjne, saa lad dine Trælle faa dette Land i Eje; før os ikke over Jordan!«
6 Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
Men Moses sagde til Gaditerne og Rubeniterne: »Skal eders Brødre drage i Krig, medens I bliver boende her?
7 Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
Og hvorfor vil I betage Israeliterne Modet til at drage over til det Land, HERREN har givet dem?
8 Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
Det gjorde eders Fædre, da jeg fra Kadesj-Barnea sendte dem hen for at se paa Landet;
9 Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
da de var draget op til Esjkoldalen og havde set paa Landet, det og de Israeliterne Modet til at drage ind i det Land, HERREN havde givet dem.
10 A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
Men HERRENS Vrede blussede den Gang op, og han svor:
11 ‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
De Mænd, der er draget op fra Ægypten, fra Tyveaarsalderen og opefter, skal ikke faa det Land at se, jeg tilsvor Abraham, Isak og Jakob, fordi de ikke viste mig fuld Lydighed,
12 ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
med Undtagelse af Kenizziten Kaleb, Jefunnes Søn, og Josua, Nuns Søn, thi de viste HERREN fuld Lydighed!
13 Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
Og HERRENS Vrede blussede op mod Israel, og han lod dem vanke om i Ørkenen i fyrretyve Aar, indtil hele den Slægt var gaaet til Grunde, der gjorde, hvad der var ondt i HERRENS Øjne.
14 “Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
Og se, I træder nu i eders Fædres Fodspor, en Yngel af Syndere, for yderligere at øge HERRENS Vrede mod Israel!
15 In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
Naar I viger bort fra ham, vil han lade det blive endnu længer i Ørkenen, og I bringer Fordærvelse over hele dette Folk.«
16 Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
Da traadte de frem for ham og sagde: »Vi vil kun bygge Kvægfolde til vore Hjorde her og Byer til vore Familier;
17 Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
men selv vil vi ruste os til Kamp og drage i Spidsen for Israeliterne, til vi har bragt dem hen til deres Sted; imens skal vore Familier blive i de befæstede Byer i Ly for Landets Indbyggere.
18 Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
Vi vil ikke vende tilbage til vore Huse, før enhver af Israeliterne har faaet sin Arvelod;
19 Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
thi vi vil ikke have Arvelod sammen med dem paa den anden Side af Jordan og længere borte, eftersom vi har faaet vor Arvelod her paa denne Side af Jordan paa Østsiden.«
20 Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
Da sagde Moses til dem: »Hvis I gør det, hvis I ruster eder til Kamp for HERRENS Aasyn,
21 in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
hvis alle eders kamprustede Mænd overskrider Jordan for HERRENS Aasyn og bliver der, indtil han har jaget sine Fjender bort fra sit Aasyn,
22 to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
og hvis I først vender tilbage, naar Landet er undertvunget for HERRENS Aasyn, skal I være sagesløse over for HERREN og Israel, og saa skal Landet her blive eders Ejendom for HERRENS Aasyn.
23 “Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
Men hvis I ikke gør det, se, da synder I mod HERREN, og da skal I faa eders Synd at mærke, den skal nok finde eder.
24 Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
Byg eder Byer til eders Familier og Folde til eders Smaakvæg og gør, som I har sagt!«
25 Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
Da sagde Gaditerne og Rubeniterne til Moses: »Dine Trælle vil gøre, som min Herre byder;
26 ’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
vore Børn, Kvinder, Hjorde og alt vort Kvæg skal blive der i Gileads Byer,
27 Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
men dine Trælle vil drage over og tage Del i Krigen, saa mange som er rustet til Kamp for HERRENS Aasyn, saaledes som min Herre har sagt.«
28 Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
Saa gav Moses Præsten Eleazar og Josua, Nuns Søn, og Overhovederne for de israelitiske Stammers Fædrenehuse Befaling om dem,
29 ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
og Moses sagde til dem: »Hvis Gaditerne og Rubeniterne, saa mange som er rustet til Kamp for HERRENS Aasyn, gaar over Jordan sammen med eder og Landet bliver eder underlagt, skal I give dem Gilead i Eje;
30 Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
men hvis de ikke gaar over sammen med eder, rustede til Kamp, skal de have Bopæl anvist blandt eder i Kana'ans Land.«
31 Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
Da svarede Gaditerne og Rubeniterne: »Hvad HERREN har talt til dine Trælle, vil vi gøre;
32 Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
vi vil, rustede til Kamp for HERRENS Øjne, drage over til Kana'ans Land, men vor Arvelod paa den anden Side af Jordan bliver i vort Eje.«
33 Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
Da gav Moses Gaditerne, Rubeniterne og Josefs Søn Manasses halve Stamme Amoriterkongen Sihons Kongerige og Kong Og af Basans Kongerige, Landet med Byerne og deres Omraade, Landets Byer rundt om.
34 Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
Saa byggede Gaditerne Dibon, Atarot, Aroer.
35 Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
Atarot-Sjofan, Ja'zer, Jogbeha,
36 Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
Bet-Nimra, Bet-Haran, befæstede Byer, og Kvægfolde;
37 Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
og Rubeniterne byggede Hesjbon, El'ale og Kirjatajim,
38 haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
Nebo og Ba'al-Meon, hvis Navne ændredes, og Sibma; og de opkaldte Byerne, som de byggede, efter deres Navne.
39 Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
Og Manasses Søn Makirs Sønner drog til Gilead og erobrede det og drev de der boende Amoriter bort;
40 Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
og Moses overdrog Gilead til Manasses Søn Makir, og han bosatte sig der;
41 Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
men Manasses Søn Ja'ir drog hen og erobrede deres Teltbyer og kaldte dem Ja'irs Teltbyer.
42 Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.
Og Noba drog hen og erobrede Kenat med tilhørende Smaabyer og kaldte det Noba efter sit eget Navn.

< Ƙidaya 32 >