< Ƙidaya 31 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
RAB Musa'ya, “Midyanlılar'dan İsrailliler'in öcünü al; sonra ölüp atalarına kavuşacaksın” dedi.
2 “Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3 Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
Bunun üzerine Musa halka, “Midyanlılar'a karşı savaşmak ve onlardan RAB'bin öcünü almak üzere aranızdan adamlar silahlandırın” dedi,
4 Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
“Savaşa İsrail'in her oymağından bin kişi gönderin.”
5 Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
Böylece İsrail'in her oymağından biner kişi olmak üzere 12 000 kişi seçilip savaşa hazırlandı.
6 Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
Musa onları –her oymaktan biner kişiyi– ve Kâhin Elazar oğlu Pinehas'ı savaşa gönderdi. Pinehas yanına kutsal yere ait bazı eşyaları ve çağrı borazanlarını aldı.
7 Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
RAB'bin Musa'ya verdiği buyruk uyarınca, Midyanlılar'a savaş açıp bütün erkekleri öldürdüler.
8 A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
Öldürdükleri arasında beş Midyan kralı –Evi, Rekem, Sur, Hur ve Reva– da vardı. Beor oğlu Balam'ı da kılıçla öldürdüler.
9 Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
Midyanlı kadınlarla çocuklarını tutsak alıp bütün hayvanlarını, sürülerini, mallarını yağmaladılar.
10 Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
Midyanlılar'ın yaşadığı bütün kentleri, obaları ateşe verdiler.
11 Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
İnsanları, hayvanları, yağmalanmış bütün malları yanlarına aldılar.
12 suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
Tutsaklarla yağmalanmış malları Şeria Irmağı'nın yanında, Eriha karşısında, Moav ovalarındaki ordugahta konaklayan Musa'yla Kâhin Elazar'a ve İsrail topluluğuna getirdiler.
13 Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
Musa, Kâhin Elazar ve topluluğun önderleri onları karşılamak için ordugahın dışına çıktılar.
14 Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
Musa savaştan dönen ordu komutanlarına –binbaşılara, yüzbaşılara– öfkelendi.
15 Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
Onlara, “Bütün kadınları sağ mı bıraktınız?” diye çıkıştı,
16 Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
“Bu kadınlar Balam'ın verdiği öğüde uyarak Peor olayında İsrailliler'in RAB'be ihanet etmesine neden oldular. Bu yüzden RAB'bin topluluğu arasında ölümcül hastalık başgösterdi.
17 Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
Şimdi bütün erkek çocukları ve erkekle yatmış kadınları öldürün.
18 amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
Yalnız erkekle yatmamış genç kızları kendiniz için sağ bırakın.
19 “Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
“Aranızda birini öldüren ya da öldürülen birine dokunan herkes yedi gün ordugahın dışında kalsın. Üçüncü ve yedinci gün kendinizi de tutsaklarınızı da günahtan arındıracaksınız.
20 Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
Her giysiyi, deriden, keçi kılından, tahtadan yapılmış her nesneyi arındıracaksınız.”
21 Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
Bundan sonra Kâhin Elazar, savaştan dönen askerlere, “RAB'bin Musa'ya buyurduğu yasanın kuralı şudur” dedi,
22 Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
“Altını, gümüşü, tuncu, demiri, kalayı, kurşunu –ateşe dayanıklı her nesneyi– ateşten geçireceksiniz; ancak bundan sonra temiz sayılacak. Ayrıca temizlenme suyuyla da arındıracaksınız. Ateşe dayanıklı olmayan nesneleri sudan geçireceksiniz.
23 da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
24 A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
Yedinci gün giysilerinizi yıkayın. Böylece temiz sayılacaksınız. Sonra ordugaha girebilirsiniz.”
25 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
RAB Musa'ya şöyle dedi:
26 “Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
“Sen, Kâhin Elazar ve topluluğun aile başları ele geçirilen insanlarla hayvanları sayacaksınız.
27 Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
Ele geçirilenleri savaşa katılan askerlerle topluluğun geri kalanı arasında paylaştıracaksınız.
28 Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
Savaşa katılan askerlere düşen paydan –insan, sığır, eşek, davardan– vergi olarak RAB'be beş yüzde bir pay ayıracaksın.
29 Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
Bu vergiyi askerlere düşen yarı paydan alacak, RAB'be armağan olarak Kâhin Elazar'a vereceksin.
30 Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
Öbür İsrailliler'e düşen yarıdan, gerek insanlardan, gerek hayvanlardan –sığır, eşek, davardan– ellide birini alıp RAB'bin Konutu'nun hizmetinden sorumlu olan Levililer'e vereceksin.”
31 Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Musa'yla Kâhin Elazar RAB'bin Musa'ya buyurduğu gibi yaptılar.
32 Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
Savaşa katılan askerlerin ele geçirdiklerinden kalanlar şunlardı: 675 000 davar,
33 shanu 72,000
72 000 sığır,
34 da jakuna 61,000.
61 000 eşek,
35 Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
erkekle yatmamış 32 000 kız.
36 Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
Savaşa katılan askerlere düşen yarı pay da şuydu: 337 500 davar,
37 tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
bunlardan RAB'be vergi olarak 675 davar verildi;
38 shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
36 000 sığır, bunlardan RAB'be vergi olarak 72 sığır verildi;
39 jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
30 500 eşek, bunlardan RAB'be vergi olarak 61 eşek verildi;
40 mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
16 000 kişi, bunlardan RAB'be vergi olarak 32 kişi verildi.
41 Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Musa, RAB'bin kendisine buyurduğu gibi, RAB'be ayrılan vergiyi Kâhin Elazar'a verdi.
42 Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
Musa'nın savaşa katılan askerlerden alıp İsrailliler'e ayırdığı yarı pay şuydu:
43 kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
Topluluğa düşen yarı pay 337 500 davar,
44 shanu 36,000,
36 000 sığır,
45 jakuna 30,500
30 500 eşek,
46 da mutane 16,000.
16 000 kişi.
47 Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
Musa, RAB'bin kendisine buyurduğu gibi, İsrailliler'e düşen yarı paydan her elli kişiden ve hayvandan birini alıp RAB'bin Konutu'nun hizmetinden sorumlu olan Levililer'e verdi.
48 Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
Ordu komutanları –binbaşılar ve yüzbaşılar– Musa'ya gidip,
49 suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
“Efendimiz, yönetimimiz altındaki askerleri saydık, eksik yok” dediler,
50 Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
“İşte, ele geçirdiğimiz altın eşyaları –pazıbentleri, bilezikleri, yüzükleri, küpeleri, kolyeleri– getirdik. Günahlarımızı bağışlatmak için bunları RAB'be sunuyoruz.”
51 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
Musa'yla Kâhin Elazar altını, her tür işlenmiş altın eşyayı onlardan aldılar.
52 Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
Binbaşı ve yüzbaşılardan alıp RAB'be armağan olarak sundukları altının toplam ağırlığı 16 750 şekeldi.
53 Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
Savaşa katılan her asker kendine yağmalanmış maldan almıştı.
54 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.
Musa'yla Kâhin Elazar binbaşı ve yüzbaşılardan aldıkları altını İsrailliler için RAB'bin önünde bir anımsatma sunusu olarak Buluşma Çadırı'na getirdiler.

< Ƙidaya 31 >