< Ƙidaya 31 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse, et dit:
2 “Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
« Venge les enfants d'Israël sur les Madianites. Ensuite, vous serez rassemblés auprès de votre peuple. »
3 Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
Moïse parla au peuple, et dit: « Armez des hommes parmi vous pour la guerre, afin qu'ils aillent contre Madian, pour exécuter la vengeance de Yahvé sur Madian.
4 Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
Vous enverrez mille hommes de chaque tribu, de toutes les tribus d'Israël, à la guerre. »
5 Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
On livra donc, parmi les milliers d'Israël, mille hommes de chaque tribu, soit douze mille hommes armés pour la guerre.
6 Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
Moïse les envoya, mille de chaque tribu, à la guerre, avec Phinées, fils du prêtre Éléazar, à la guerre, les ustensiles du sanctuaire et les trompettes d'alarme dans sa main.
7 Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Ils combattirent contre Madian, comme Yahvé l'avait ordonné à Moïse. Ils tuèrent tous les mâles.
8 A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
Ils tuèrent les rois de Madian avec le reste de leurs morts: Evi, Rékem, Tsur, Hur et Réba, les cinq rois de Madian. Ils tuèrent aussi par l'épée Balaam, fils de Beor.
9 Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
Les enfants d'Israël emmenèrent captives les femmes de Madian et leurs petits enfants, et ils pillèrent tout leur bétail, tous leurs troupeaux et tous leurs biens.
10 Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
Ils brûlèrent au feu toutes leurs villes, dans les lieux qu'ils habitaient, et tous leurs campements.
11 Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
Ils prirent tous les captifs et tout le butin, tant des hommes que des animaux.
12 suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
Ils amenèrent les captifs, avec le butin et le pillage, à Moïse, au sacrificateur Éléazar et à l'assemblée des enfants d'Israël, au camp des plaines de Moab, qui sont près du Jourdain, à Jéricho.
13 Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
Moïse et le sacrificateur Éléazar, avec tous les chefs de l'assemblée, sortirent à leur rencontre hors du camp.
14 Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
Moïse se mit en colère contre les officiers de l'armée, les chefs de milliers et les chefs de centaines, qui venaient du service de la guerre.
15 Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
Moïse leur dit: « Avez-vous sauvé toutes les femmes en vie?
16 Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
Voici qu'elles ont poussé les enfants d'Israël, par le conseil de Balaam, à commettre une infidélité à l'égard de l'Éternel dans l'affaire de Péor, et c'est ainsi que la plaie a frappé la congrégation de l'Éternel.
17 Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
Maintenant, tuez tout mâle parmi les petits enfants, et tuez toute femme qui a connu un homme en couchant avec lui.
18 amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
Mais toutes les filles qui n'ont pas connu d'homme en couchant avec lui, gardez-les vivantes pour vous.
19 “Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
« Campez hors du camp pendant sept jours. Celui qui a tué quelqu'un et celui qui a touché un mort, purifiez-vous le troisième jour et le septième jour, vous et vos captifs.
20 Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
Vous purifierez tout vêtement, tout ce qui est fait en peau, tout ce qui est fait en poil de chèvre et tout ce qui est fait en bois. »
21 Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
Le sacrificateur Éléazar dit aux hommes de guerre qui allaient au combat: « Voici le règlement de la loi que l'Éternel a prescrite à Moïse.
22 Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
Cependant, l'or, l'argent, l'airain, le fer, l'étain et le plomb,
23 da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
tout ce qui peut résister au feu, vous le ferez passer par le feu, et il sera pur; néanmoins, il sera purifié avec l'eau pour être impur. Tout ce qui ne résistera pas au feu, vous le ferez passer dans l'eau.
24 A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
Tu laveras tes vêtements le septième jour, et tu seras pur. Ensuite, tu entreras dans le camp. »
25 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
L'Éternel parla à Moïse, et dit:
26 “Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
Comptez le butin qui a été fait, tant pour les hommes que pour les animaux, vous, le prêtre Éléazar et les chefs de famille de l'assemblée,
27 Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
et partagez le butin en deux parties: entre les hommes de guerre qui sont allés au combat et toute l'assemblée.
28 Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
Prélève un tribut à l'Éternel sur les hommes de guerre qui sont allés au combat: une âme sur cinq cents, sur les personnes, sur le bétail, sur les ânes et sur les troupeaux.
29 Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
Prenez-en la moitié et donnez-la au prêtre Éléazar, pour l'offrande de l'Éternel.
30 Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
Sur la moitié des enfants d'Israël, tu prendras une personne tirée sur cinquante, du bétail, des ânes et des troupeaux, de tout le bétail, et tu la donneras aux Lévites, qui font le service de la tente de Yahvé. »
31 Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Moïse et le prêtre Éléazar firent ce que l'Éternel avait ordonné à Moïse.
32 Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
Or le butin, en sus du butin que les hommes de guerre avaient pris, fut de six cent soixante-quinze mille brebis,
33 shanu 72,000
soixante-douze mille têtes de bétail,
34 da jakuna 61,000.
soixante et un mille ânes,
35 Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
et trente-deux mille personnes en tout, des femmes qui n'avaient pas connu d'homme en couchant avec lui.
36 Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
La moitié, qui était la part de ceux qui partaient pour la guerre, était en nombre de trois cent trente-sept mille cinq cents moutons;
37 tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
et le tribut de l'Éternel sur les moutons était de six cent soixante-quinze.
38 shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
Les bovins étaient au nombre de trente-six mille, et le tribut de l'Éternel était de soixante-douze.
39 jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
Les ânes étaient au nombre de trente mille cinq cents; le tribut de l'Éternel était de soixante et un.
40 mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
Les personnes étaient au nombre de seize mille; le tribut de l'Éternel était de trente-deux personnes.
41 Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Moïse remit au sacrificateur Éléazar le tribut, qui était l'ondoiement de l'Éternel, comme l'Éternel l'avait ordonné à Moïse.
42 Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
Sur la moitié des enfants d'Israël, que Moïse sépara des hommes qui avaient combattu
43 kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
(la moitié de l'assemblée était de trois cent trente-sept mille cinq cents moutons,
44 shanu 36,000,
trente-six mille têtes de bétail,
45 jakuna 30,500
trente mille cinq cents ânes
46 da mutane 16,000.
et seize mille personnes),
47 Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
sur la moitié des enfants d'Israël, Moïse prit un homme et un animal sur cinquante, et les donna aux Lévites, qui faisaient le service du tabernacle de Yahvé, comme Yahvé l'avait ordonné à Moïse.
48 Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
Les officiers qui commandaient les milliers de l'armée, les chefs de milliers et les chefs de centaines, s'approchèrent de Moïse.
49 suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
Ils dirent à Moïse: « Tes serviteurs ont fait le compte des hommes de guerre qui sont sous nos ordres, et il ne manque pas un seul homme parmi nous.
50 Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
Nous avons apporté l'offrande de l'Éternel, ce que chacun a trouvé: des ornements en or, des bracelets, des bagues, des anneaux, des boucles d'oreilles et des colliers, pour faire l'expiation de nos âmes devant l'Éternel. »
51 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
Moïse et le sacrificateur Éléazar prirent leur or, tous les bijoux travaillés.
52 Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
Tout l'or de l'ondoiement qu'ils offrirent à l'Éternel, des chefs de milliers et des chefs de centaines, fut de seize mille sept cent cinquante sicles.
53 Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
Les hommes de guerre avaient fait du butin, chacun pour soi.
54 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.
Moïse et le prêtre Éléazar prirent l'or des chefs de milliers et des chefs de centaines, et l'apportèrent dans la tente d'assignation, comme souvenir pour les enfants d'Israël devant l'Éternel.

< Ƙidaya 31 >