< Ƙidaya 31 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And he spoke Yahweh to Moses saying.
2 “Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
Avenge [the] vengeance of [the] people of Israel from with the Midianites (after *L(P)*) you will be gathered to people your.
3 Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
And he spoke Moses to the people saying be equipped from with you men for war so they may be on Midian to give [the] vengeance of Yahweh on Midian.
4 Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
One thousand to the tribe one thousand to the tribe for all [the] tribes of Israel you will send out to war.
5 Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
And they were selected from [the] thousands of Israel one thousand to the tribe two [plus] ten thousand armed [men] of war.
6 Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
And he sent them Moses one thousand to the tribe to war them and Phinehas [the] son of Eleazar the priest to war and [the] vessels of the holy place and [the] trumpets of the alarm [were] in hand his.
7 Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And they waged war on Midian just as he had commanded Yahweh Moses and they killed every male.
8 A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
And [the] kings of Midian they killed with slain [ones] their Evi and Rekem and Zur and Hur and Reba [the] five [the] kings of Midian and Balaam [the] son of Beor they killed with the sword.
9 Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
And they took captive [the] people of Israel [the] women of Midian and little one[s] their and all cattle their and all livestock their and all wealth their they plundered.
10 Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
And all cities their in dwelling places their and all encampments their they burned with fire.
11 Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
And they took all the plunder and all the booty among humankind and among the livestock.
12 suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
And they brought to Moses and to Eleazar the priest and to [the] congregation of [the] people of Israel the captive[s] and the booty and the plunder to the camp to [the] plains of Moab which [were] at [the] Jordan of Jericho.
13 Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
And they went out Moses and Eleazar the priest and all [the] leaders of the congregation to meet them to from [the] outside of the camp.
14 Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
And he was angry Moses towards [the] officers of the army [the] commanders of the thousands and [the] commanders of the hundreds who were coming from [the] war of the battle.
15 Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
And he said to them Moses ¿ have you let live every female.
16 Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
There! they they were to [the] people of Israel by [the] word of Balaam to offer unfaithfulness in Yahweh on [the] matter of Peor and it was the plague among [the] congregation of Yahweh.
17 Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
And therefore kill every male among the little one[s] and every woman [who has] known a man to [the] lying of a male kill.
18 amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
And all the little one[s] among the women who not they have known lying of a male preserve alive for yourselves.
19 “Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
And you encamp from [the] outside of the camp seven days any [one who] has killed anyone and any - [one who] has touched the [one] slain you will purify yourselves on the day third and on the day seventh you and captive[s] your.
20 Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
And every garment and every article of hide and every product of goat hair and every article of wood you will purify yourselves.
21 Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
And he said Eleazar the priest to [the] men of the army who had gone to the battle this [is] [the] statute of the law which he commanded Yahweh Moses.
22 Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
Only the gold and the silver the bronze the iron the tin and the lead.
23 da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
Every thing which it will go in the fire you will make pass in the fire and it will be pure nevertheless by [the] water of impurity it will purify itself and all that not it will go in the fire you will make pass in the water.
24 A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
And you will wash clothes your on the day seventh and you will be pure and after you will come to the camp.
25 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
And he said Yahweh to Moses saying.
26 “Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
Lift up [the] head of [the] booty of captivity among humankind and among the livestock you and Eleazar the priest and [the] leaders of [the] fathers of the congregation.
27 Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
And you will divide the booty between [those] skilled of the battle who went out to war and between all the congregation.
28 Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
And you will raise a tax for Yahweh from with [the] men of war who went out to war one person from [the] five hundred from humankind and from the cattle and from the donkeys and from the sheep.
29 Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
From half their you will take [it] and you will give [it] to Eleazar the priest [the] contribution of Yahweh.
30 Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
And from [the] half of [the] people of Israel you will take - one - [person] drawn from the fifty from humankind from the cattle from the donkeys and from the sheep from all the livestock and you will give them to the Levites [who] keep [the] service of [the] tabernacle of Yahweh.
31 Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And he did Moses and Eleazar the priest just as he had commanded Yahweh Moses.
32 Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
And it was the booty [the] remainder of the plunder which they had plundered [the] people of the army sheep six hundred thousand and seventy thousand and five thousand.
And cattle two and seventy thousand.
And donkeys one and sixty thousand.
35 Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
And [the] person[s] of humankind from the women who not they had known lying of a male every person two and thirty thousand.
36 Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
And it was the half [the] portion of those [who] had gone out in the army [the] number of the sheep [was] three hundred thousand and thirty thousand and seven thousand and five hundred.
37 tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
And it was the tax for Yahweh from the sheep six hundred five and seventy.
38 shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
And the cattle [were] six and thirty thousand and tax their for Yahweh [was] two and seventy.
39 jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
And donkeys [were] thirty thousand and five hundred and tax their for Yahweh [was] one and sixty.
40 mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
And [the] person[s] of humankind [were] six-teen thousand and tax their for Yahweh [was] two and thirty person[s].
41 Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And he gave Moses [the] tax of [the] contribution of Yahweh to Eleazar the priest just as he had commanded Yahweh Moses.
42 Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
And from [the] half of [the] people of Israel which he had divided Moses from the men who had gone to war.
43 kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
And it was [the] half of the congregation from the sheep three hundred thousand and thirty thousand seven thousand and five hundred.
And cattle six and thirty thousand.
And donkeys thirty thousand and five hundred.
And person[s] of humankind six-teen thousand.
47 Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
And he took Moses from [the] half of [the] people of Israel those drawn one from the fifty from humankind and from the livestock and he gave them to the Levites [who] keep [the] service of [the] tabernacle of Yahweh just as he had commanded Yahweh Moses.
48 Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
And they drew near to Moses the officers who [were] of [the] thousands of the army [the] commanders of the thousands and [the] commanders of the hundreds.
49 suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
And they said to Moses servants your they have lifted up [the] head of [the] men of war who [were] in hand our and not he is missing from us anyone.
50 Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
And we have brought near [the] offering of Yahweh everyone [that] which he found an article of gold an armlet and a bracelet a signet-ring an earring and an ornament to make atonement on selves our before Yahweh.
51 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
And he took Moses and Eleazar the priest the gold from with them every article of work.
52 Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
And it was - all [the] gold of the contribution which they raised for Yahweh six-teen thousand seven hundred and fifty shekel[s] from with [the] commanders of the thousands and from with [the] commanders of the hundreds.
53 Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
[the] men of The army they had taken plunder everyone for himself.
54 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.
And he took Moses and Eleazar the priest the gold from with [the] commanders of the thousands and the hundreds and they brought it into [the] tent of meeting a memorial for [the] people of Israel before Yahweh.