< Ƙidaya 31 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying:
2 “Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
Revenge first the children of Israel on the Madianites, and so thou shalt be gathered to thy people.
3 Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
And Moses forthwith said: Arm of you men to fight, who may take the revenge of the Lord on the Madianites.
4 Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
Let a thousand men be chosen out of every tribe of Israel to be sent to the war.
5 Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
And they gave a thousand of every tribe, that is to say, twelve thousand men well appointed for battle.
6 Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
And Moses sent them with Phinees the son of Eleazar the priest, and he delivered to him the holy vessels, and the trumpets to sound.
7 Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And when they had fought against the Madianites and had overcome them, they slew all the men.
8 A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
And their kings Evi, and Recem, and Sur, and Hur, and Rebe, five princes of the nation: Balaam also the son of Beer they killed with the sword.
9 Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
And they took their women, and their children captives, and all their cattle, and all their goods: and all their possessions they plundered:
10 Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
And all their cities, and their villages, and castles, they burned.
11 Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
And they carried away the booty, and all that they had taken both of men and of beasts.
12 suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
And they brought them to Moses, and Eleazar the priest, and to all the multitude of the children of Israel. But the rest of the things for use they carried to the camp on the plains of Moab, beside the Jordan over against Jericho.
13 Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
And Moses and Eleazar the priest and all the princes of the synagogue went forth to meet them without the camp.
14 Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
And Moses being angry with the chief officers of the army, the tribunes, and the centurions that were come from the battle,
15 Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
Said: Why have you saved the women?
16 Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
Are not these they, that deceived the children of Israel by the counsel of Balaam, and made you transgress against the Lord by the sin of Phogor, for which also the people was punished?
17 Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
Therefore kill all that are of the male sex, even of the children: and put to death the women, that have carnally known men.
18 amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
But the girls, and all the women that are virgins save for yourselves:
19 “Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
And stay without the camp seven days. He that hath killed a man, or touched one that is killed, shall be purified the third day and the seventh day.
20 Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
And of all the spoil, every garment, or vessel, or any thing made for use, of the skins, or hair of goats, or of wood, shall be purified.
21 Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
Eleazar also the priest spoke to the men of the army, that had fought, in this manner: This is the ordinance of the law, which the Lord hath commanded Moses:
22 Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
Gold, and silver, and brass, and iron, and lend, and tin,
23 da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
And all that may pass through the fire, shall be purified by fire, but whatsoever cannot abide the fire, shall be sanctified with the water of expiation:
24 A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
And you shall wash your garments the seventh day, and being purified, you shall afterwards enter into the camp.
25 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
And the Lord said to Moses:
26 “Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
Take the sum of the things that were taken both of man and beast, thou and Eleazar the priest and the princes of the multitude:
27 Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
And thou shalt divide the spoil equally, between them that fought and went out to the war, and between the rest of the multitude.
28 Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
And thou shalt separate a portion to the Lord from them that fought and were in the battle, one soul of five hundred as well of persons as of oxen and asses and sheep.
29 Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
And thou shalt give it to Eleazar the priest, because they are the firstfruits of the Lord.
30 Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
Out of the moiety also of the children of Israel thou shalt take the fiftieth head of persons, and of oxen, and asses, and sheep, and of all beasts, and thou shalt give them to the Levites that watch in the charge of the tabernacle of the Lord.
31 Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And Moses and Eleazar did as the Lord had commanded.
32 Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
And the spoil which the army had taken, was six hundred seventy-five thousand sheep,
Seventy-two thousand oxen,
Sixty-one thousand asses:
35 Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
And thirty-two thousand persons of the female sex, that had not known men.
36 Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
And one half was given to them that had been in the battle, to wit, three hundred thirty-seven thousand five hundred sheep:
37 tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
Out of which, for the portion of the Lord, were reckoned six hundred seventy-five sheep.
38 shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
And out of the thirty-six thousand oxen, seventy-two oxen:
39 jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
Out of the thirty thousand five hundred asses, sixty-one asses:
40 mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
Out of the sixteen thousand persons, there fell to the portion of the Lord, thirty-two souls.
41 Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And Moses delivered the number of the firstfruits of the Lord to Eleazar the priest, as had been commanded him,
42 Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
Out of the half of the children of Israel, which he had separated for them that had been in the battle.
43 kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
But out of the half that fell to the rest of the multitude, that is to say, out of the three hundred thirty-seven thousand five hundred sheep,
And out of the thirty-six thousand oxen,
And out of the thirty thousand five hundred asses,
And out of the sixteen thousand persons,
47 Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
Moses took the fiftieth head, and gave it to the Levites that watched in the tabernacle of the Lord, as the Lord had commanded.
48 Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
And when the commanders of the army, and the tribunes and centurions were come to Moses, they said:
49 suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
We thy servants have reckoned up the number of the fighting men, whom we had under our hand, and not so much as one was wanting.
50 Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
Therefore we offer as gifts to the Lord what gold every one of us could find in the booty, in garters and tablets, rings and bracelets, and chains, that thou mayst pray to the Lord for us.
51 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
And Moses and Eleazar the priest received all the gold in divers kinds,
52 Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
In weight sixteen thousand seven hundred and fifty sicles, from the tribunes and from the centurions.
53 Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
For that which every one had taken in the booty was his own.
54 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.
And that which was received they brought into the tabernacle of the testimony, for a memorial of the children of Israel before the Lord.