< Ƙidaya 31 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then the Lord said to Moses,
2 “Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
Give the Midianites punishment for the wrong they did to the children of Israel: and after that you will go to rest with your people.
3 Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
So Moses said to the people, Let men from among you be armed for war to put into effect against Midian the Lord's punishment on them.
4 Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
From every tribe of Israel send a thousand to the war.
5 Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
So from the thousands of Israel a thousand were taken from every tribe, twelve thousand men armed for war.
6 Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
And Moses sent them out to war, a thousand from every tribe, and with them Phinehas, the son of Eleazar the priest, taking in his hands the vessels of the holy place and the horns for sounding the note of war.
7 Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And they made war on Midian, as the Lord gave orders to Moses; and they put to death every male.
8 A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
They put the kings of Midian to death with the rest, Evi and Reken and Zur and Hur and Reba, the five kings of Midian: and Balaam, the son of Beor, they put to death with the sword.
9 Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
The women of Midian with their little ones the children of Israel took prisoner; and all their cattle and flocks and all their goods they took for themselves;
10 Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
And after burning all their towns and all their tent-circles,
11 Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
They went away with the goods they had taken, man and beast.
12 suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
And the prisoners and the goods and everything they had taken, they took to Moses and Eleazar the priest and the people of Israel, to the tent-circle in the lowlands of Moab by the Jordan at Jericho.
13 Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
Then Moses and Eleazar the priest and the chiefs of the people went out to them before they had come into the tent-circle.
14 Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
And Moses was angry with the chiefs of the army, the captains of thousands and the captains of hundreds who had come back from the war.
15 Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
And Moses said to them, Why have you kept all the women safe?
16 Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
It was these who, moved by Balaam, were the cause of Israel's sin against the Lord in the question of Peor, because of which disease came on the people of the Lord.
17 Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
So now put every male child to death, and every woman who has had sex relations with a man.
18 amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
But all the female children who have had no sex relations with men, you may keep for yourselves.
19 “Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
You yourselves will have to keep outside the tent-circle for seven days, anyone of you who has put any person to death or come near a dead body; and on the third day and on the seventh day make yourselves and your prisoners clean.
20 Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
And every bit of clothing, and anything made of leather or goats' hair or wood, you are to make clean.
21 Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
Then Eleazar the priest said to the men of war who had been to the fight, This is the rule of the law which the Lord has given to Moses:
22 Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
But gold and silver and brass and iron and tin and lead,
23 da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
And anything which may be heated, is to go through the fire and be made clean; but in addition it is to be put in the water of cleaning: and anything which may not go through the fire is to be put in the water.
24 A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
And on the seventh day, after washing your clothing, you will be clean, and then you may come into the tent-circle.
25 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
And the Lord said to Moses,
26 “Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
Get an account of everything which was taken in the war, of man and of beast, you and Eleazar the priest and the heads of families of the people:
27 Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
And let division be made of it into two parts, one for the men of war who went out to the fight, and one for all the people:
28 Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
And from the men of war who went out let there be offered to the Lord one out of every five hundred, from the persons, and from the oxen and asses and sheep:
29 Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
Take this from their part and give it to Eleazar the priest as an offering to be lifted up to the Lord.
30 Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
And from the part given to the children of Israel, take one out of every fifty, from the persons, and from the oxen and asses and sheep, and give it to the Levites who have the care of the House of the Lord.
31 Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
So Eleazar and Moses did as the Lord had given orders to Moses.
32 Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
Now the beasts taken, in addition to what the fighting-men took for themselves, were six hundred and seventy-five thousand sheep,
And seventy-two thousand oxen,
And sixty-one thousand asses;
35 Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
And thirty-two thousand persons, that is, women who had never had sex relations with a man.
36 Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
And the half given as their part to the men who went to the war, was three hundred and thirty-seven thousand, five hundred sheep,
37 tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
Of which the Lord's part was six hundred and seventy-five.
38 shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
The number of oxen was thirty-six thousand, of which the Lord's part was seventy-two;
39 jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
The number of asses was thirty thousand, five hundred, of which the Lord's part was sixty-one.
40 mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
And the number of persons was sixteen thousand, of which the Lord's part was thirty-two persons.
41 Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And Moses gave the Lord's part, lifted up as an offering, to Eleazar the priest, as the Lord had given orders to Moses.
42 Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
And from the half given to the children of Israel, which Moses had kept separate from that given to the fighting-men,
43 kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
(Now the people's half was three hundred and thirty-seven thousand, five hundred sheep,
And thirty-six thousand oxen,
And thirty thousand, five hundred asses,
And sixteen thousand persons; )
47 Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
Even from the children of Israel's half, Moses took one out of every fifty, men and beasts, and gave them to the Levites who had the care of the House of the Lord; as the Lord gave orders to Moses.
48 Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
Then the men in authority over the thousands of the army, the captains of thousands and captains of hundreds, came to Moses,
49 suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
And said to him, Your servants have taken note of the number of all the fighting-men under our orders, and every one is present;
50 Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
And we have here an offering for the Lord from what every man took in the war, ornaments of gold, leg-chains and arm-rings, finger-rings, ear-rings, and neck-ornaments, to make our souls free from sin before the Lord.
51 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
So Moses and Eleazar the priest took the gold from them, even all the worked ornaments.
52 Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
And the gold which the captains of thousands and captains of hundreds gave, as an offering to be lifted up before the Lord, came to sixteen thousand, seven hundred and fifty shekels.
53 Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
(For every man of the army had taken goods for himself in the war.)
54 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.
Then Moses and Eleazar the priest took the gold given by the captains of thousands and captains of hundreds, and took it into the Tent of meeting, to be a sign in memory of the children of Israel before the Lord.