< Ƙidaya 30 >

1 Musa ya ce wa shugabannin kabilan Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.
And Moses speaketh unto the heads of the tribes of the sons of Israel, saying, 'This [is] the thing which Jehovah hath commanded:
2 Sa’ad da mutum ya yi wa Ubangiji alkawari, ko kuwa ya rantse zai yi wani abu, kada yă ƙi cika maganarsa, amma yă cika kome da ya faɗa.
'When a man voweth a vow to Jehovah, or hath sworn an oath to bind a bond on his soul, he doth not pollute his word; according to all that is going out from his mouth he doth.
3 “Sa’ad da yarinya, wadda har yanzu tana a gidan mahaifinta ta yi wa Ubangiji alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
'And when a woman voweth a vow to Jehovah, and hath bound a bond in the house of her father in her youth,
4 mahaifinta kuwa ya ji alkawarin da ta yi, bai kuma ce mata kome ba, to, sai alkawarin da ta yi da wa’adinta su tabbata.
and her father hath heard her vow, and her bond which she hath bound on her soul, and her father hath kept silent at her, then have all her vows been established, and every bond which she hath bound on her soul is established.
5 Amma in mahaifinta ya hana ta, sa’ad da ya ji game da shi, to, ba wani daga cikin alkawari ko rantsuwar da ta yi zai tabbata; Ubangiji kuwa zai gafarta mata domin maihaifinta ya hana ta.
'And if her father hath disallowed her in the day of his hearing, none of her vows and her bonds which she hath bound on her soul is established, and Jehovah is propitious to her, for her father hath disallowed her.
6 “In ta yi aure, sai daga baya ta yi alkawari ko kuwa leɓunanta sun furta alkawari da garaje, cewa za tă yi wani abu,
'And if she be at all to a husband, and her vows [are] on her, or a wrongful utterance [on] her lips, which she hath bound on her soul,
7 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, to, alkawarin da ta yi da kuma rantsuwar da ta yi, su tabbata.
and her husband hath heard, and in the day of his hearing, he hath kept silent at her, then have her vows been established, and her bonds which she hath bound on her soul are established.
8 Amma in mijin ya hana ta sa’ad da ya ji, zai warware alkawari da kuma rantsuwar da ta yi da garaje, Ubangiji kuwa zai gafarce ta.
'And if in the day of her husband's hearing he disalloweth her, then he hath broken her vow which [is] on her, and the wrongful utterance of her lips which she hath bound on her soul, and Jehovah is propitious to her.
9 “Duk wani alkawari ko rantsuwar da gwauruwa, ko macen da aurenta ya mutu, ta yi, zai tabbata a kanta.
'As to the vow of a widow or cast-out woman, all that she hath bound on her soul is established on her.
10 “In macen aure ta yi alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
'And if [in] the house of her husband she hath vowed, or hath bound a bond on her soul with an oath,
11 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, bai kuma hana ta ba, to, dukan alkawari da kuma rantsuwar da ta yi su tabbata a kanta.
and her husband hath heard, and hath kept silent at her — he hath not disallowed her — then have all her vows been established, and every bond which she hath bound on her soul is established.
12 Amma in mijin ya warware su sa’ad da ya ji, to, ba wani alkawari ko rantsuwar da ya fito daga leɓunanta da zai tabbata. Mijinta ya warware su, Ubangiji kuma zai gafarce ta.
'And if her husband doth certainly break them in the day of his hearing, none of the outgoing of her lips concerning her vows, or concerning the bond of her soul, is established — her husband hath broken them — and Jehovah is propitious to her.
13 Mijinta yana iya tabbatar, ko yă rushe duk wani alkawari ko rantsuwar da ta ɗauka.
'Every vow and every oath — a bond to humble a soul — her husband doth establish it, or her husband doth break it;
14 Amma in mijinta bai ce mata kome ba, to, ya tabbatar da dukan alkawarinta da kuma rantsuwarta ke nan. Ya tabbatar da su ta wurin yin shiru sa’ad da ya ji ta.
and if her husband certainly keep silent at her, from day unto day, then he hath established all her vows, or all her bonds which [are] upon her; he hath established them, for he hath kept silent at her in the day of his hearing;
15 Amma in ya ji, sa’an nan daga baya ya hana ta, to, zai sha hukuncin laifinta.”
and if he doth at all break them after his hearing, then he hath borne her iniquity.'
16 Waɗannan su ne ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Musa game da dangantakar miji da matarsa, da kuma tsakanin mahaifi da’yarsa wadda har yanzu tana a gidansa.
These [are] the statutes which Jehovah hath commanded Moses between a man and his wife, between a father and his daughter, in her youth, [in] the house of her father.

< Ƙidaya 30 >