< Ƙidaya 30 >

1 Musa ya ce wa shugabannin kabilan Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.
Moses spoke to the leaders of the tribes of the people of Israel. He said, “This is what Yahweh has commanded.
2 Sa’ad da mutum ya yi wa Ubangiji alkawari, ko kuwa ya rantse zai yi wani abu, kada yă ƙi cika maganarsa, amma yă cika kome da ya faɗa.
When anyone makes a vow to Yahweh, or swears an oath to bind himself with a promise, he must not break his word. He must keep his promise to do everything that comes out of his mouth.
3 “Sa’ad da yarinya, wadda har yanzu tana a gidan mahaifinta ta yi wa Ubangiji alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
When a young woman living in her father's house makes a vow to Yahweh and binds herself with a promise,
4 mahaifinta kuwa ya ji alkawarin da ta yi, bai kuma ce mata kome ba, to, sai alkawarin da ta yi da wa’adinta su tabbata.
if her father hears the vow and the promise by which she has bound herself, and if he says nothing to reverse her, then all her vows will remain in force. Every promise by which she has bound herself will remain in force.
5 Amma in mahaifinta ya hana ta, sa’ad da ya ji game da shi, to, ba wani daga cikin alkawari ko rantsuwar da ta yi zai tabbata; Ubangiji kuwa zai gafarta mata domin maihaifinta ya hana ta.
But if her father hears about her vow and her promise, and if he says nothing to her, then all the vows and promises that she took on herself will remain in force.
6 “In ta yi aure, sai daga baya ta yi alkawari ko kuwa leɓunanta sun furta alkawari da garaje, cewa za tă yi wani abu,
However, if her father hears all the vows she made and her solemn promises with which she has bound herself, and if he overrules her on that same day, then they will not remain in force. Yahweh will forgive her because her father had overruled her.
7 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, to, alkawarin da ta yi da kuma rantsuwar da ta yi, su tabbata.
If she marries a man while she is under those vows, or if she makes rash promises with which she obligates herself, those obligations will remain in force.
8 Amma in mijin ya hana ta sa’ad da ya ji, zai warware alkawari da kuma rantsuwar da ta yi da garaje, Ubangiji kuwa zai gafarce ta.
But if her husband stops her on the day that he hears about it, then he cancels the vow that she has made, the rash talk of her lips with which she has bound herself. Yahweh will release her.
9 “Duk wani alkawari ko rantsuwar da gwauruwa, ko macen da aurenta ya mutu, ta yi, zai tabbata a kanta.
But as for a widow or a divorced woman, everything by which she has bound herself will remain in force against her.
10 “In macen aure ta yi alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
If a woman made a vow in her husband's house or obligates herself by taking an oath,
11 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, bai kuma hana ta ba, to, dukan alkawari da kuma rantsuwar da ta yi su tabbata a kanta.
and her husband hears of it, but he says nothing to her and he does oppose her, then all her vows must stand and the obligations she made must remain in force.
12 Amma in mijin ya warware su sa’ad da ya ji, to, ba wani alkawari ko rantsuwar da ya fito daga leɓunanta da zai tabbata. Mijinta ya warware su, Ubangiji kuma zai gafarce ta.
But if her husband cancels them on the day that he heard about them, then whatever came out of her lips about her vows or promises will not remain in force. Her husband has canceled them. Yahweh will release her.
13 Mijinta yana iya tabbatar, ko yă rushe duk wani alkawari ko rantsuwar da ta ɗauka.
Every vow or oath a woman takes that binds her to deny herself something may be confirmed or canceled by her husband.
14 Amma in mijinta bai ce mata kome ba, to, ya tabbatar da dukan alkawarinta da kuma rantsuwarta ke nan. Ya tabbatar da su ta wurin yin shiru sa’ad da ya ji ta.
But if he says nothing at all to her day after day, then he confirms all her vows and binding promises that she has made. He has confirmed them because he has said nothing to her at the time that he heard about them.
15 Amma in ya ji, sa’an nan daga baya ya hana ta, to, zai sha hukuncin laifinta.”
If her husband tries to cancel his wife's vow a long time after he has heard about it, then he will be responsible for her sin.”
16 Waɗannan su ne ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Musa game da dangantakar miji da matarsa, da kuma tsakanin mahaifi da’yarsa wadda har yanzu tana a gidansa.
These are the statutes that Yahweh commanded Moses to announce—statutes for what is between a man and his wife and between a father and his daughter when she is in her youth in her father's family.

< Ƙidaya 30 >