< Ƙidaya 30 >

1 Musa ya ce wa shugabannin kabilan Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.
And he said to the leaders of the tribes of the sons of Israel: “This is the word, which the Lord has instructed:
2 Sa’ad da mutum ya yi wa Ubangiji alkawari, ko kuwa ya rantse zai yi wani abu, kada yă ƙi cika maganarsa, amma yă cika kome da ya faɗa.
If any man makes a vow to the Lord, or binds himself by an oath, he shall not make his word null and void, but all that he has promised, he shall fulfill.
3 “Sa’ad da yarinya, wadda har yanzu tana a gidan mahaifinta ta yi wa Ubangiji alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
If a woman, who is in her father’s house, vows anything, or binds herself by an oath, and she is still in a state of childhood, if her father knew of the vow which she has promised or of the oath by which she has obligated her soul, and he kept silent, she shall be liable to the vow:
4 mahaifinta kuwa ya ji alkawarin da ta yi, bai kuma ce mata kome ba, to, sai alkawarin da ta yi da wa’adinta su tabbata.
whatever she has promised or swore, she shall complete in deed.
5 Amma in mahaifinta ya hana ta, sa’ad da ya ji game da shi, to, ba wani daga cikin alkawari ko rantsuwar da ta yi zai tabbata; Ubangiji kuwa zai gafarta mata domin maihaifinta ya hana ta.
But if her father, as soon as he had heard it, had contradicted it, both her vows and her oaths shall be nullified, neither shall she be held liable to the promise, because her father had contradicted it.
6 “In ta yi aure, sai daga baya ta yi alkawari ko kuwa leɓunanta sun furta alkawari da garaje, cewa za tă yi wani abu,
If she has a husband, and she has vowed anything, then, once the word has gone out of her mouth, she will have obligated her soul by an oath.
7 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, to, alkawarin da ta yi da kuma rantsuwar da ta yi, su tabbata.
On the day that her husband will hear of it, and yet not contradict it, she shall be liable to the vow, and she shall repay whatever she has promised.
8 Amma in mijin ya hana ta sa’ad da ya ji, zai warware alkawari da kuma rantsuwar da ta yi da garaje, Ubangiji kuwa zai gafarce ta.
But if, as soon as he hears it, he contradicts it, then he will have caused her promises, and the words by which she had bound her soul, to be null and void. The Lord will be favorable to her.
9 “Duk wani alkawari ko rantsuwar da gwauruwa, ko macen da aurenta ya mutu, ta yi, zai tabbata a kanta.
Widows and divorced women shall repay whatever they have vowed.
10 “In macen aure ta yi alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
If a wife in the house of her husband has bound herself by a vow or an oath,
11 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, bai kuma hana ta ba, to, dukan alkawari da kuma rantsuwar da ta yi su tabbata a kanta.
if her husband heard it and remained silent, and he did not contradict the promise, she shall repay what she had promised.
12 Amma in mijin ya warware su sa’ad da ya ji, to, ba wani alkawari ko rantsuwar da ya fito daga leɓunanta da zai tabbata. Mijinta ya warware su, Ubangiji kuma zai gafarce ta.
But if he promptly contradicts it, she shall not be held liable to the promise. For her husband has contradicted it. And the Lord will be favorable to her.
13 Mijinta yana iya tabbatar, ko yă rushe duk wani alkawari ko rantsuwar da ta ɗauka.
If she has vowed or bound herself by oath, in order to afflict her soul by fasting, or by abstaining from other things, it shall be for the arbitration of her husband, as to whether or not she may do it.
14 Amma in mijinta bai ce mata kome ba, to, ya tabbatar da dukan alkawarinta da kuma rantsuwarta ke nan. Ya tabbatar da su ta wurin yin shiru sa’ad da ya ji ta.
But if the husband, upon hearing it, remains silent, and he delays judgment until another day, whatever she had vowed or promised, she shall repay, because when he first heard it, he remained silent.
15 Amma in ya ji, sa’an nan daga baya ya hana ta, to, zai sha hukuncin laifinta.”
And if he contradicted it only sometime after he had known about it, he shall bear his iniquity.”
16 Waɗannan su ne ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Musa game da dangantakar miji da matarsa, da kuma tsakanin mahaifi da’yarsa wadda har yanzu tana a gidansa.
These are the laws which the Lord has appointed to Moses, between a husband and a wife, between a father and a daughter, who is still in the state of childhood or who remains in her father’s house.

< Ƙidaya 30 >