< Ƙidaya 30 >
1 Musa ya ce wa shugabannin kabilan Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.
And Moses said to the heads of the tribes of the children of Israel, This is the order of the Lord.
2 Sa’ad da mutum ya yi wa Ubangiji alkawari, ko kuwa ya rantse zai yi wani abu, kada yă ƙi cika maganarsa, amma yă cika kome da ya faɗa.
When a man takes an oath to the Lord, or gives an undertaking having the force of an oath, let him not go back from his word, but let him do whatever he has said he will do.
3 “Sa’ad da yarinya, wadda har yanzu tana a gidan mahaifinta ta yi wa Ubangiji alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
If a woman, being young and under the authority of her father, takes an oath to the Lord or gives an undertaking;
4 mahaifinta kuwa ya ji alkawarin da ta yi, bai kuma ce mata kome ba, to, sai alkawarin da ta yi da wa’adinta su tabbata.
If her father, hearing of her oath or the undertaking she has given, says nothing to her, then all her oaths and every undertaking she has given will have force.
5 Amma in mahaifinta ya hana ta, sa’ad da ya ji game da shi, to, ba wani daga cikin alkawari ko rantsuwar da ta yi zai tabbata; Ubangiji kuwa zai gafarta mata domin maihaifinta ya hana ta.
But if her father, hearing of it, makes her take back her word, then the oaths or the undertakings she has given will have no force; and she will have forgiveness from the Lord, because her oath was broken by her father.
6 “In ta yi aure, sai daga baya ta yi alkawari ko kuwa leɓunanta sun furta alkawari da garaje, cewa za tă yi wani abu,
And if she is married to a husband at the time when she is under an oath or an undertaking given without thought;
7 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, to, alkawarin da ta yi da kuma rantsuwar da ta yi, su tabbata.
If her husband, hearing of it, says nothing to her at the time, then the oaths she made and the undertakings she gave will have force.
8 Amma in mijin ya hana ta sa’ad da ya ji, zai warware alkawari da kuma rantsuwar da ta yi da garaje, Ubangiji kuwa zai gafarce ta.
But if her husband, hearing of it, makes her take it back, then the oath she made and the undertaking she gave without thought will have no force or effect, and she will have the Lord's forgiveness.
9 “Duk wani alkawari ko rantsuwar da gwauruwa, ko macen da aurenta ya mutu, ta yi, zai tabbata a kanta.
But an oath made by a widow or one who is no longer married to her husband, and every undertaking she has given, will have force.
10 “In macen aure ta yi alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
If she made an oath while she was under the authority of her husband,
11 mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, bai kuma hana ta ba, to, dukan alkawari da kuma rantsuwar da ta yi su tabbata a kanta.
And her husband, hearing of it, said nothing to her and did not put a stop to it, then all her oaths and every undertaking she gave will have force.
12 Amma in mijin ya warware su sa’ad da ya ji, to, ba wani alkawari ko rantsuwar da ya fito daga leɓunanta da zai tabbata. Mijinta ya warware su, Ubangiji kuma zai gafarce ta.
But if her husband, on hearing of it, made them without force or effect, then whatever she has said about her oaths or her undertaking has no force: her husband has made them without effect, and she will have the Lord's forgiveness.
13 Mijinta yana iya tabbatar, ko yă rushe duk wani alkawari ko rantsuwar da ta ɗauka.
Every oath, and every undertaking which she gives, to keep herself from pleasure, may be supported or broken by her husband.
14 Amma in mijinta bai ce mata kome ba, to, ya tabbatar da dukan alkawarinta da kuma rantsuwarta ke nan. Ya tabbatar da su ta wurin yin shiru sa’ad da ya ji ta.
But if the days go on, and her husband says nothing whatever to her, then he is giving the support of his authority to her oaths and undertakings, because at the time of hearing them he said nothing to her.
15 Amma in ya ji, sa’an nan daga baya ya hana ta, to, zai sha hukuncin laifinta.”
But if at some time after hearing of them, he makes them without force, then he is responsible for her wrongdoing.
16 Waɗannan su ne ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Musa game da dangantakar miji da matarsa, da kuma tsakanin mahaifi da’yarsa wadda har yanzu tana a gidansa.
These are the laws which the Lord gave Moses in relation to a man and his wife, or a father and a young daughter who is under his authority.