< Ƙidaya 3 >

1 Waɗannan su ne zuriyar Haruna da Musa a lokacin da Ubangiji ya yi magana da Musa a kan Dutsen Sinai.
Voici les générations d’Aaron et de Moïse, au jour que le Seigneur parla à Moïse sur la montagne de Sinaï.
2 Sunayen’ya’yan Haruna su ne, Nadab ɗan fari, da Abihu, da Eleyazar da Itamar.
Et voici les noms des fils d’Aaron: Son premier-né Nadab, ensuite Abiu, Eléazar et Ithamar.
3 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Haruna, shafaffun firistocin da aka naɗa domin su yi aiki firist.
Tels sont les noms des fils d’Aaron, prêtres qui furent oints, et dont les mains furent remplies et consacrées pour qu’ils exerçassent les fonctions du sacerdoce.
4 Amma Nadab da Abihu suka fāɗi suka mutu a gaban Ubangiji a Hamadar Sinai a sa’ad da suka ƙona turare da haramtacciyar wuta a gabansa. Ba su kuwa da’ya’ya; saboda haka Eleyazar da Itamar kaɗai suka yi aiki firist a zamanin mahaifinsu Haruna.
Or Nadab et Abiu moururent sans enfants lorsqu’ils offraient un feu étranger en la présence du Seigneur dans le désert de Sinaï; et Eléazar et Ithamar exercèrent les fonctions du sacerdoce devant Aaron leur père.
5 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et le Seigneur parla à Moïse, disant:
6 “Ka kawo mutanen Lawi, ka kuma gabatar da su ga Haruna firist, don su taya shi aiki.
Fais approcher la tribu de Lévi, et fais-les tenir en la présence d’Aaron, le prêtre, afin qu’ils le servent, et qu’ils veillent;
7 Za su yi wa Haruna da dukan al’umma aikace-aikace a Tentin Sujada, ta wurin yin aikin tabanakul.
Qu’ils observent aussi tout ce qui appartient au culte de la multitude devant le tabernacle de témoignage;
8 Za su lura da dukan kayayyakin Tentin Sujada, suna cika hakkin Isra’ilawa ta wurin yin aiki a tabanakul.
Qu’ils gardent les vases du tabernacle, servant pour son ministère.
9 Ka ba da Lawiyawa ga Haruna da’ya’yansa; su ne za su zama Isra’ilawan da za a ba da su ɗungum gare shi.
Et tu donneras en dons les Lévites
10 Ka naɗa Haruna da’ya’yansa su yi aiki firistoci; duk wanda ya yi shisshigi a wuri mai tsarki kuwa dole a kashe shi.”
À Aaron et à ses fils auxquels ils ont été accordés par les enfants d’Israël. Mais tu établiras Aaron et ses fils dans les fonctions du sacerdoce. L’étranger qui approchera pour exercer le ministère, mourra.
11 Ubangiji ya kuma ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
12 “Ga shi na ɗauki Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a maimakon ɗan fari na kowace mace a Isra’ila. Lawiyawa nawa ne,
J’ai pris les Lévites d’entre les enfants d’Israël, à la place de tout premier-né qui ouvre un sein parmi les enfants d’Israël, et les Lévites seront à moi.
13 gama duk’ya’yan fari nawa ne. Lokacin da karkashe duk’ya’yan fari a Masar, na keɓe wa kaina kowane ɗan fari a Isra’ila, ko mutum, ko dabba. Za su zama nawa. Ni ne Ubangiji.”
Car tout premier-né est à moi, depuis que j’ai frappé les premiers-nés dans la terre d’Egypte, j’ai consacré pour moi tout ce qui naît le premier en Israël, depuis l’homme jusqu’à la bête: Je suis le Seigneur.
14 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai ya ce,
Le Seigneur parla de nouveau à Moïse dans le désert de Sinaï, disant:
15 “Ka ƙidaya Lawiyawa bisa ga iyalansu da kabilarsu. Ka ƙidaya kowane ɗan jinjiri mai wata ɗaya ko fiye.”
Dénombre les enfants de Lévi, selon les maisons de leurs pères et leurs familles, tout mâle d’un mois et au-dessus.
16 Saboda haka Musa ya ƙidaya su duka, kamar yadda maganar Ubangiji ta umarta.
Moïse les dénombra, comme avait ordonné le Seigneur,
17 Ga sunayen’ya’yan Lawi, Gershon, Kohat da Merari.
Et furent trouvés les enfants de Lévi, selon leurs noms, Gerson, Caath et Mérari.
18 Ga sunayen mutanen Gershon, Libni, da Shimeyi
Les fils de Gerson: Lebni et Séméi.
19 Sunayen mutanen Kohat kuwa su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.
Les fils de Caath: Amram, Jésaar, Hébron et Oziel.
20 Dangin Merari su ne. Mali da Mushi. Ga kabilan Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Les fils de Mérari: Moholi et Musi.
21 A wajen Gershonawa, kabilarsa su ne Libniyawa, da Shimeyiyawa; waɗannan su ne mutanen Gershom.
De Gerson sont sorties deux familles, la Lebnitique et la Séméitique,
22 Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya zuwa gaba da haihuwa su kai 7,500.
Dont la population du sexe masculin depuis un mois et au-dessus dénombrée, fut de sept mille cinq cents.
23 Kabilar Gershonawa za su yi sansani ta fuskar yamma, a bayan tabanakul.
Ceux-ci camperont derrière le tabernacle, vers l’occident,
24 Eliyasaf ɗan Layel shi ne shugaban iyalan Gershonawa.
Sous le prince Eliasaph, fils de Laël.
25 A Tentin Sujada, Gershonawa su ne za su lura da mazauni da tabanakul da kuma tentin, abubuwan rufensa, labule a ƙofar Tentin Sujada,
Et ils auront la garde dans le tabernacle d’alliance,
26 da labulen filin da yake kewaye da tabanakul da kuma bagade, da igiyoyi, da kuma kowane abin da ya danganci aikinsu.
Du tabernacle lui-même et de sa couverture, du voile qu’on tire devant la porte du toit d’alliance, et des rideaux du parvis, ainsi que du voile qui est suspendu à l’entrée du parvis du tabernacle, et de tout ce qui appartient au ministère de l’autel, les cordages du tabernacle et tous ses ustensiles.
27 Kabilar Kohat su ne, Amramawa da Izharawa da Hebronawa da Uzziyelawa; waɗannan su ne kabilar Kohatawa.
La parenté de Caath aura les peuples Amramites, Jésaarites, Hébronites et Oziélites. Ce sont là les familles des Caathites recensées selon leurs noms.
28 Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya ko fiye, 8,600 ne. Kohatawa ne suke lura da wuri mai tsarki.
Tous ceux du genre masculin depuis un mois et au-dessus, huit mille six cents auront la garde du sanctuaire,
29 Kohatawa za su yi sansani a kudu da tabanakul.
Et ils camperont vers le côté méridional;
30 Shugaban kabilar Kohatawa shi ne Elizafan ɗan Uzziyel.
Et leur prince sera Elisaphan, fils d’Oziel.
31 Su ne da hakkin kula da akwatin alkawari, tebur, wurin ajiye fitila, bagade, kayayyakin wuri mai tsarki da ake amfani da su a sujada, labule, da kuma kome da ya danganci aikinsu.
Ainsi ils garderont l’arche, la table, le chandelier, les autels, les vases du sanctuaire avec lesquels se fait le service, le voile et tous les objets semblables:
32 Babban shugaban Lawiyawa shi ne Eleyazar ɗan Haruna, firist. An naɗa shi a kan waɗanda suke kula da wuri mai tsarki.
Mais le prince des princes des Lévites, Eléazar fils d’Aaron le prêtre, sera au-dessus de ceux qui veilleront à la garde du sanctuaire.
33 Kabilar Merari su ne Maliyawa da Mushiyawa; waɗannan su ne kabilar Merari.
Mais de Mérari sortiront les familles Moholites et Musites, recensées selon leurs noms.
34 Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya ko fiye, 6,200 ne.
Tous les mâles depuis un mois et au-dessus sont au nombre de six mille deux cents.
35 Shugaban iyalan Merari shi ne Zuriyel ɗan Abihayil. Za su yi sansani arewa da tabanakul.
Leur prince est Suriel, fils d’Abihaïel: c’est au côté septentrional qu’ils camperont.
36 Kabilar Merari ne aka sa su lura da katakan tabanakul, sandunanta, dogayen sandunanta, tarukanta, dukan kayan aiki da kowane abin da ya danganci aikinsu,
Seront sous leur garde: les ais du tabernacle, les leviers, les colonnes et leurs soubassements, et tout ce qui appartient à un tel service;
37 da ginshiƙai kewaye da filin tare da rammuka da turaku da igiyoyinsu.
Et les colonnes autour du parvis avec leurs soubassements, et les pieux avec leurs cordages.
38 Musa da Haruna da’ya’yansu za su yi sansani gabas da tabanakul, wajen fitowar rana; a gaban Tentin Sujada. Su ne da hakkin lura da wuri mai tsarki a madadin Isra’ilawa. Duk wani wanda ba ya wannan aiki, ya kuma kusaci wuri mai tsarki, za a kashe shi.
Devant le tabernacle d’alliance, c’est-à-dire vers le côté oriental, camperont Moïse et Aaron avec ses fils, ayant la garde du sanctuaire, au milieu des enfants d’Israël; tout étranger qui s’en approchera, mourra.
39 Jimillar Lawiyawan da Musa da Haruna suka ƙidaya bisa ga umarnin Ubangiji bisa ga danginsu, haɗe da kowane jariri daga wata ɗaya ko fiye, 22,000 ne.
Tous les Lévites que dénombrèrent Moïse et Aaron d’après le commandement du Seigneur, selon leurs familles, parmi les mâles d’un mois et au-dessus, furent vingt-deux mille.
40 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ƙidaya dukan’ya’yan fari na Isra’ilawa maza daga wata ɗaya da kuma fiye ka kuma rubuta sunayensu.
Le Seigneur dit encore à Moïse: Dénombre les premiers-nés mâles d’entre les enfants d’Israël, depuis un mois et au-dessus, et tu en tiendras compte.
41 Ka ɗauko mini Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari na Isra’ilawa, haka ma na dabbobi na Lawiyawa, a maimakon’ya’yan fari na dabbobin Isra’ilawa. Ni ne Ubangiji.”
Et tu prendras pour moi les Lévites à la place de tout premier-né des enfants d’Israël; je suis le Seigneur; et leurs bestiaux à la place de tous les premiers-nés des bestiaux des enfants d’Israël.
42 Haka Musa ya ƙidaya’ya’yan fari na Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
Moïse recensa, comme avait ordonné le Seigneur, les premiers-nés des enfants d’Israël;
43 Jimillar’ya’yan fari maza daga wata ɗaya da kuma fiye, da aka rubuta bisa ga sunayensu, 22,273 ne.
Et les mâles, selon leurs noms, depuis un mois et au-dessus, furent vingt-deux mille deux cent soixante-treize.
44 Sai Ubangiji ya kuma yi magana da Musa ya ce,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
45 “Ka ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari na Isra’ila, dabbobin Lawiyawa kuma a maimakon dabbobinsu. Lawiyawa za su zama nawa. Ni ne Ubangiji.
Prends les Lévites à la place des premiers-nés des enfants d’Israël, et les bestiaux des Lévites à la place de leurs bestiaux, et les Lévites seront à moi. Je suis le Seigneur.
46 Don a fanshi’ya’yan fari 273 na Isra’ilawa da suka fi Lawiyawa yawa,
Et pour le prix des deux cent soixante-treize d’entre les premiers-nés des enfants d’Israël qui dépassent le nombre des Lévites,
47 ka karɓi shekel biyar domin kowannensu, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, wanda yake da nauyin gera ashirin.
Tu prendras cinq sicles pour chaque tête, selon la mesure du sanctuaire. Le sicle a vingt oboles.
48 Ka ba wa Haruna da’ya’yansa kuɗin fansar da ya haura kai na’ya’yan farin Isra’ilawa.”
Et tu donneras l’argent à Aaron pour le prix de ceux qui sont de plus.
49 Haka, Musa ya karɓi kuɗin fansar waɗanda suka haura yawan Lawiyawa.
Moïse prit donc l’argent de ceux qui étaient de plus, et qu’ils avaient rachetés des Lévites,
50 Daga’ya’yan fari na Isra’ilawa, ya karɓi azurfa masu nauyin shekel 1,365, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri.
Pour les premiers-nés des enfants d’Israël, mille trois cent soixante-cinq sicles selon le poids du sanctuaire;
51 Sa’an nan Musa ya ba da kuɗin fansar ga Haruna da’ya’yansa, yadda maganar Ubangiji ta umarce shi.
Et il le donna à Aaron et à ses fils, selon la parole que lui avait ordonnée le Seigneur.

< Ƙidaya 3 >