< Ƙidaya 27 >

1 ’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
Alors s’approchèrent les filles de Celofhad, fils de Héfer, fils de Ghilad, fils de Makhir, fils de Manassé, de la descendance de Manassé, fils de Joseph, lesquelles filles avaient nom Mailla, Noa, Hogla, Milca et Tirça;
2 Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
elles se présentèrent devant Moïse, devant Eléazar le pontife, devant les phylarques et toute la communauté, à l’entrée de la tente d’assignation, disant:
3 “Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
"Notre père est mort dans le désert. Toutefois, il ne faisait point partie de cette faction liguée contre le Seigneur, de la faction de Coré: c’est pour son péché qu’il est mort, et il n’avait point de fils.
4 Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
Faut-il que le nom de notre père disparaisse du milieu de sa famille, parce qu’il n’a pas laissé de fils? Donne-nous une propriété parmi les frères de notre père!"
5 Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
Moïse déféra leur cause à l’Éternel.
6 Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
Et l’Éternel parla ainsi à Moïse:
7 “Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
"Les filles de Celofhad ont raison. Tu dois leur accorder un droit d’hérédité parmi les frères de leur père, et leur transmettre l’héritage de leur père.
8 “Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
Et tu parleras en ces termes aux enfants d’Israël: Si un homme meurt sans laisser de fils, vous ferez passer son héritage à sa fille.
9 In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
S’Il n’a pas de fille, vous donnerez son héritage à ses frères.
10 In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
S’Il n’a pas de frères, vous donnerez son héritage aux frères de son père.
11 In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
Et si son père n’a pas laissé de frères, vous donnerez son héritage au plus proche parent qu’il aura dans sa famille, lequel en deviendra possesseur. Ce sera pour les enfants d’Israël une règle de droit, ainsi que l’Éternel l’a prescrit à Moïse."
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
L’Éternel dit à Moïse: "Monte sur cette hauteur des Abarîm, pour contempler le pays que j’ai donné aux enfants d’Israël.
13 Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
Quand tu l’auras contemplé, tu iras rejoindre tes pères, toi aussi, comme l’a fait Aaron ton frère;
14 gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
parce que vous avez contrevenu à ma parole dans le désert de Cîn, lors de la querelle soulevée par la communauté, au lieu de faire éclater devant eux ma sainteté par les eaux." Ce sont les eaux de Meribath-Kadêch, au désert de Cîn.
15 Musa ya ce wa Ubangiji,
Alors Moïse parla à l’Éternel en ces termes:
16 “Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
"Que l’Éternel, le Dieu des esprits de toute chair, institue un chef sur cette communauté,
17 yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
qui marche sans cesse à leur tête et qui dirige tous leurs mouvements, afin que la communauté de l’Éternel ne soit pas comme un troupeau sans pasteur."
18 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
Et l’Éternel dit à Moïse: "Fais approcher de toi Josué, fils de Noun, homme animé de mon esprit, et impose ta main sur lui.
19 Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
Tu le mettras en présence d’Eléazar le pontife et de toute la communauté, et lui donneras ses instructions devant eux.
20 Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
Tu lui communiqueras une partie de ta majesté, afin que toute l’assemblée des enfants d’Israël lui obéisse.
21 Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
II devra se présenter devant le pontife Eléazar, qui interrogera pour lui l’oracle des Ourîm devant le Seigneur: c’est à sa voix qu’ils partiront, à sa voix qu’ils rentreront, lui-même aussi bien que tous les enfants d’Israël et toute la communauté."
22 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
Moïse fit comme l’Éternel lui avait prescrit: il prit Josué, le mit en présence du pontife Eléazar et de toute la communauté,
23 Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
lui imposa les mains et lui donna ses instructions, comme l’Éternel l’avait dit par l’organe de Moïse.

< Ƙidaya 27 >