< Ƙidaya 27 >

1 ’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
Et les filles de Tselophkhad, fils de Hépher, fils de Galaad, fils de Makir, fils de Manassé, des familles de Manassé, fils de Joseph, s’approchèrent (et ce sont ici les noms de ses filles: Makhla, Noa, et Hogla, et Milca, et Thirtsa);
2 Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
et elles se tinrent devant Moïse et devant Éléazar, le sacrificateur, et devant les princes et toute l’assemblée, à l’entrée de la tente d’assignation, disant:
3 “Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
Notre père est mort dans le désert, et il n’était pas dans l’assemblée de ceux qui s’ameutèrent contre l’Éternel, dans l’assemblée de Coré; mais il est mort dans son péché, et il n’a pas eu de fils.
4 Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
Pourquoi le nom de notre père serait-il retranché du milieu de sa famille parce qu’il n’a pas de fils? Donne-nous une possession au milieu des frères de notre père.
5 Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
Et Moïse apporta leur cause devant l’Éternel.
6 Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
7 “Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
Les filles de Tselophkhad ont bien parlé. Tu leur donneras une possession d’héritage au milieu des frères de leur père, et tu feras passer à elles l’héritage de leur père.
8 “Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
Et tu parleras aux fils d’Israël, disant: Quand un homme mourra sans avoir de fils, vous ferez passer son héritage à sa fille.
9 In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
Et s’il n’a pas de fille, vous donnerez son héritage à ses frères.
10 In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
Et s’il n’a pas de frères, vous donnerez son héritage aux frères de son père.
11 In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
Et s’il n’y a pas de frères de son père, vous donnerez son héritage à son parent qui, de sa famille, lui est le plus proche, et il le possédera. Et ce sera pour les fils d’Israël un statut de droit, comme l’Éternel a commandé à Moïse.
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
Et l’Éternel dit à Moïse: Monte sur cette montagne d’Abarim, et regarde le pays que j’ai donné aux fils d’Israël.
13 Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
Tu le regarderas, et tu seras recueilli vers tes peuples, toi aussi, comme Aaron, ton frère, a été recueilli;
14 gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
parce que, au désert de Tsin, lors de la contestation de l’assemblée, vous avez été rebelles à mon commandement, quand vous auriez dû me sanctifier à leurs yeux à l’occasion des eaux: ce sont là les eaux de Meriba à Kadès, dans le désert de Tsin.
15 Musa ya ce wa Ubangiji,
Et Moïse parla à l’Éternel, disant:
16 “Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
Que l’Éternel, le Dieu des esprits de toute chair, établisse sur l’assemblée un homme
17 yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
qui sorte devant eux et entre devant eux, et qui les fasse sortir et les fasse entrer; et que l’assemblée de l’Éternel ne soit pas comme un troupeau qui n’a pas de berger.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
Et l’Éternel dit à Moïse: Prends Josué, fils de Nun, un homme en qui est l’Esprit, et pose ta main sur lui.
19 Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
Et tu le feras se tenir devant Éléazar, le sacrificateur, et devant toute l’assemblée, et tu lui donneras des ordres devant leurs yeux;
20 Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
et tu mettras sur lui de ta gloire, afin que toute l’assemblée des fils d’Israël l’écoute.
21 Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
Et il se tiendra devant Éléazar, le sacrificateur, qui interrogera pour lui les jugements d’urim devant l’Éternel: à sa parole ils sortiront, et à sa parole ils entreront, lui et tous les fils d’Israël avec lui, toute l’assemblée.
22 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
Et Moïse fit comme l’Éternel lui avait commandé; et il prit Josué et le fit se tenir devant Éléazar, le sacrificateur, et devant toute l’assemblée.
23 Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Et il posa ses mains sur lui, et lui donna des ordres, comme l’Éternel l’avait dit par Moïse.

< Ƙidaya 27 >