< Ƙidaya 27 >

1 ’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
One day the five daughters of Zelophehad came [to Moses/me]. They were Mahlah, Noah, Hoglah, Milcah, and Tirzah.
2 Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
They came to the entrance of the Sacred Tent and stood in front of Eleazar, Moses/me, the tribal leaders, and many [EUP] other Israeli people.
3 “Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
They said, “Our father died [during the time that we were] in the desert, and he did not have any sons. But he was not among those who supported Korah, who rebelled against Yahweh. He died just because he was a sinner [like everyone else].
4 Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
(Why should the name of his clan disappear [with the result that we do not receive any land] only because our father had no sons?/It is not right that the name of his clan disappear [with the result that we do not receive any land] only because our father had no sons.) [RHQ] So give us some land like our relatives will be getting!”
5 Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
So Moses/I asked Yahweh [what to do about] their request.
6 Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
And Yahweh replied,
7 “Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
“What the daughters of Zelophehad are requesting is right. You must give them some land, just as you are giving to their father’s relatives. Give to each of them some of the land that would have been given to their brothers [if they had any].
8 “Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
“Also tell this to the Israeli people: ‘If a man who has no sons dies, give the things that his sons would have inherited to his daughters.
9 In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
If the man has no sons or daughters, give to his brothers the things that his sons and daughters would have inherited.
10 In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
If the man had no brothers, give to his father’s brothers the things that his sons or daughters or brothers would have inherited.
11 In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
If the man’s father has no brothers, give to his closest relative the things that the others would have inherited.’ That will be a rule for the Israeli people, because I am giving this as a command to you, Moses, [to tell them].”
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
One day, Yahweh said to Moses/me, “Climb to the top of the Abarim Mountains [east of the Jordan River]. Then look out over the land that I am giving to the Israeli people.
13 Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
After you have seen it, you will die [EUP] just like your [older] brother Aaron did.
14 gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
The reason [that you will die and not enter that land] is that you both disobeyed my instructions/commands in the Zin Desert. When the Israeli people rebelled against me there at Meribah, near Kadesh, [I told you to speak to the rock to cause] water to flow out of it. [But because you struck the rock instead of speaking to it], you did not show the people my holy power.”
15 Musa ya ce wa Ubangiji,
Then Moses/I said this to Yahweh:
16 “Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
“Yahweh, you are the God who directs the spirits of all people. So please appoint a new leader for the Israeli people.
17 yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
Appoint someone who will lead your people when they go to fight a battle, so that they will not [just wander around] like sheep that do not have a shepherd.” [SIM]
18 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
Yahweh replied, “Get Joshua, the son of Nun, who has my Spirit within him. Lay your hands on him [to appoint him].
19 Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
Cause him to stand in front of Eleazar the priest, as all the people are watching, and commission/appoint him to be the new leader of the Israeli people.
20 Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
Give to him some of the authority that you now have, in order that all the Israeli people will [know that they must] obey him.
21 Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
When you all need me to guide you, Joshua will stand in front of Eleazar. Then by (casting lots/throwing marked stones on the ground) Eleazar will find out what they should do.”
22 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
So Moses/I did what Yahweh commanded. He/I presented Joshua to Eleazar and to all the Israeli people.
23 Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Moses/I laid his/my hands on him and commissioned/appointed him to do the work that Yahweh told Moses/me to tell him to do.

< Ƙidaya 27 >