< Ƙidaya 27 >
1 ’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
Then drew near the daughters of Zelophehad, the son of Hepher, the son of Gilead, the son of Machir, the son of Manasseh, of the families of Manasseh the son of Joseph; and these were the names of his daughters: Mahlah, Noah, and Hoglah, and Milcah, and Tirzah.
2 Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
And they stood before Moses, and before Eleazar the priest, and before the princes and the whole assembly, at the entrance of the tent of meeting, saying,
3 “Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
Our father died in the wilderness, and he was not in the band of them that banded themselves together against Jehovah in the band of Korah; but he died in his own sin, and he had no sons.
4 Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
Why should the name of our father be taken away from his family, because he has no son? Give unto us a possession among the brethren of our father.
5 Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
And Moses brought their cause before Jehovah.
6 Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
7 “Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
The daughters of Zelophehad speak right: thou shalt surely give them a possession of an inheritance among their father's brethren; and thou shalt cause the inheritance of their father to pass unto them.
8 “Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
And unto the children of Israel shalt thou speak, saying, If a man die, and have no son, then ye shall cause his inheritance to pass unto his daughter.
9 In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
And if he have no daughter, ye shall give his inheritance unto his brethren.
10 In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
And if he have no brethren, ye shall give his inheritance unto his father's brethren.
11 In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
And if his father have no brethren, ye shall give his inheritance to his kinsman that is nearest to him in his family, and he shall possess it; and it shall be unto the children of Israel a statute of right, as Jehovah commanded Moses.
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
And Jehovah said to Moses, Get thee up into this mount Abarim, and see the land that I have given unto the children of Israel.
13 Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
And when thou hast seen it, thou also shalt be gathered unto thy peoples, as Aaron thy brother was gathered,
14 gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
because ye rebelled against my word in the wilderness of Zin, in the strife of the congregation, as to hallowing me in the matter of the water before their eyes. (That is the water of Meribah at Kadesh in the wilderness of Zin.)
15 Musa ya ce wa Ubangiji,
And Moses spoke to Jehovah, saying,
16 “Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
Let Jehovah, the God of the spirits of all flesh, set a man over the assembly,
17 yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
who may go out before them, and who may come in before them, and who may lead them out, and who may bring them in, that the assembly of Jehovah be not as sheep that have no shepherd.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
And Jehovah said to Moses, Take Joshua the son of Nun, a man in whom is the Spirit, and thou shalt lay thy hand upon him;
19 Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
and thou shalt set him before Eleazar the priest, and before the whole assembly; and give him commandment before their eyes.
20 Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
And thou shalt put of thine honour upon him, that the whole assembly of the children of Israel may obey him.
21 Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
And he shall stand before Eleazar the priest, who shall inquire for him, by the judgment of the Urim before Jehovah: at his word shall they go out, and at his word they shall come in, he, and all the children of Israel with him, even the whole assembly.
22 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
And Moses did as Jehovah had commanded him; and he took Joshua and set him before Eleazar the priest, and before the whole assembly.
23 Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
And he laid his hands upon him, and gave him commandment, as Jehovah had said through Moses.