< Ƙidaya 27 >
1 ’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
Then there approached the daughters of Zelophehad, the son of Hepher, the son of Gilead, the son of Machir, the son of Manasseh, who was the son of Joseph: and their names are Mahlah, and Noa, and Hoglah, and Milcah, and Tirzah.
2 Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
And they stood before Moses and Eleazar the priest, and all the leaders of the people, at the door of the tabernacle of the covenant, and they said:
3 “Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
“Our father died in the desert, and was not with the sedition, which was stirred up against the Lord under Korah, but he died in his own sin; he had no male sons. Why is his name taken away from his family, because he had no son? Give us a possession among the kinsmen of our father.”
4 Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
And Moses referred their case to the judgment of the Lord.
5 Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
And the Lord said to him:
6 Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
“The daughters of Zelophehad are asking for something just. So give them a possession among the kinsmen of their father, and let them succeed him in his inheritance.
7 “Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
And to the sons of Israel, you shall speak these things:
8 “Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
When a man dies without a son, his inheritance shall be transferred to his daughter.
9 In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
If he has no daughter, his brothers shall succeed him.
10 In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
But if there were also no brothers, you shall give the inheritance to the brothers of his father.
11 In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
But if he has no paternal uncles, the inheritance shall be given to those who are closest to him. And this shall be, for the sons of Israel, consecrated as a perpetual law, just as the Lord has instructed Moses.”
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
The Lord also said to Moses: “Ascend onto this mountain, Abarim, and contemplate from there the land, which I will give to the sons of Israel.
13 Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
And when you have seen it, you shall then go to your people, just as your brother Aaron went.
14 gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
For you offended me in the desert of Sin at the Contradiction of the multitude; neither were you willing to sanctify me in their sight over the waters. These are the Waters of Contradiction at Kadesh in the desert of Sin.”
15 Musa ya ce wa Ubangiji,
Moses answered him:
16 “Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
“May the Lord, the God of the spirits of all flesh, provide a man, who may be over this multitude,
17 yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
and who may be able to exit and enter before them, and who may lead them out or lead them in: lest the people of the Lord be like sheep without a shepherd.”
18 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
And the Lord said to him: “Take Joshua, the son of Nun, a man in whom the Spirit is, and place your hand upon him.
19 Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
And he shall stand before Eleazar the priest and the entire multitude.
20 Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
And you shall give him the precepts in the sight of all, and a portion of your glory, so that the entire congregation of the sons of Israel may listen to him.
21 Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
On his behalf, if anything is to be done, Eleazar the priest shall consult the Lord. He, and all the sons of Israel with him, and the rest of the multitude, shall go out and enter in at his word.”
22 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
Moses did just as the Lord had instructed. And when he had brought Joshua, he set him before Eleazar the priest, and before the entire gathering of the people.
23 Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
And imposing his hands upon his head, he repeated all that the Lord had commanded.