< Ƙidaya 26 >

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
Aconteceu pois que, depois d'aquella praga, fallou o Senhor a Moysés, e a Eleazar, filho d'Aarão o sacerdote, dizendo:
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
Tomae a somma de toda a congregação dos filhos de Israel, da edade de vinte annos e para cima, segundo as casas de seus paes: todo o que em Israel sae ao exercito.
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
Fallou-lhes pois Moysés e Eleazar o sacerdote, nas campinas de Moab, ao pé do Jordão de Jericó, dizendo:
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
Conta o povo da edade de vinte annos e para cima, como o Senhor ordenara a Moysés e aos filhos d'Israel, que sairam do Egypto.
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
Ruben, o primogenito de Israel: os filhos de Ruben foram Hanoch, do qual era a familia dos hanochitas: de Pallu a familia dos palluitas;
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
De Hezrona, familia dos hezronitas: de Carmi, a familia dos carmitas:
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
Estas são as familias dos rubenitas: e os que foram d'elles contados, foram quarenta e tres mil e setecentos e trinta.
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
E os filhos de Pallu, Eliab:
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
E os filhos d'Eliab, Nemuel, e Dathan, e Abiram: estes, Dathan e Abiram, foram os afamados da congregação, que moveram a contenda contra Moysés e contra Aarão na congregação de Coré, quando moveram a contenda contra o Senhor
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
E a terra abriu a sua bocca, e os tragou com Coré, quando morreu a congregação: quando o fogo consumiu duzentos e cincoenta homens, e foram por signal.
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
Mas os filhos de Coré não morreram.
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
Os filhos de Simeão, segundo as suas familias: de Nemuel, a familia dos nemuelitas: de Jamin, a familia dos jaminitas: de Jachin, a familia dos jachinitas:
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
De Zerah, a familia dos zerahitas: de Saul, a familia dos saulitas.
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
Estas são as familias dos simeonitas vinte e dois mil e duzentos.
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
Os filhos de Gad, segundo as suas gerações: de Zephon, a familia dos zephonitas: de Haggi, a familia dos haggitas: de Suni, a familia dos sunitas:
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
De Ozni, a familia dos oznitas: de Heri, a familia dos heritas:
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
De Arod, a familia dos aroditas: de Areli, a familia dos arelitas.
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
Estas são as familias dos filhos de Gad, segundo os que foram d'elles contados, quarenta mil e quinhentos.
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
Os filhos de Judah, Er e Onan: mas Er e Onan morreram na terra de Canaan.
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
Assim os filhos de Judah foram segundo as suas familias; de Selah a familia dos selanitas: de Pharez, a familia dos pharezitas; de Zerah, a familia dos zerahitas.
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
E os filhos de Pharez foram; de Hezron, a familia dos hezronitas: de Hamul, a familia doa hamulitas.
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
Estas são as familias de Judah, segundo os que foram d'elles contados, setenta e seis mil e quinhentos.
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
Os filhos d'Issacar, segundo as suas familias, foram; de Tola, a familia dos tolaitas: de Puva a familia dos puvitas,
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
De Jasub a familia dos jasubitas: de Simron, a familia dos simronitas.
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
Estas são as familias d'Issacar, segundo os que foram d'elles contados, sessenta e quatro mil e trezentos.
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
Os filhos de Zebulon, segundo as suas familias, foram; de Sered, a familia dos sereditas: d'Elon, a familia dos elonitas: de Jahleel, a familia dos jahleelitas.
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
Estas são as familias dos zebulonitas, segundo os que foram d'elles contados, sessenta mil e quinhentos.
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
Os filhos de José segundo as suas familias, foram Manasseh e Ephraim.
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
Os filhos de Manasseh foram; de Machir, a familia dos machiritas; e Machir gerou a Gilead: de Gilead, a familia dos gileaditas.
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
Estes são os filhos de Gilead: de Jezer, a familia dos jezeritas: de Helek, a familia das helekitas:
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
E d'Asriel, a familia dos asrielitas: e de Sechen, a familia dos sechenitas:
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
E de Semida, a familia dos semidaitas: e de Hepher, a familia dos hepheritas.
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
Porém Selofad, filho de Hepher, não tinha filhos, senão filhas: e os nomes das filhas de Selofad foram Machla, Noa, Hogla, Milca e Tirza.
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
Estas são as familias de Manasseh: e os que foram d'elles contados, foram cincoenta e dois mil e setecentos.
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
Estes são os filhos d'Ephraim, segundo as suas familias: de Sutelah, a familia dos sutelahitas: de Becher, a familia dos becheritas: de Tahan, a familia dos tahanitas.
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
E estes são os filhos de Sutelah: d'Eran, a familia dos eranitas.
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
Estas são as familias dos filhos d'Ephraim, segundo os que foram d'elles contados, trinta e dois mil e quinhentos: estes são os filhos de José, segundo as suas familias.
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
Os filhos de Benjamin, segundo as suas familias; de Bela, a familia dos belaitas: d'Asbel, a familia dos asbelitas: de Ahiram, a familia dos ahiramitas;
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
De Supham, a familia dos suphamitas: de Hupham, a familia dos huphamitas.
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
E os filhos de Bela foram Ard e Naaman: d'Ard a familia dos arditas: de Naaman a familia dos naamanitas.
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
Estes são os filhos de Benjamin, segundo as suas familias: e os que foram d'elles contados, foram quarenta e cinco mil e seiscentos.
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
Estes são os filhos de Dan, segundo as suas familias; de Suham a familia dos suhamitas: estas são as familias de Dan, segundo as suas familias.
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
Todas as familias dos suhamitas, secundo os que foram d'elles contados, foram sessenta e quatro mil e quatrocentos.
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
Os filhos d'Aser, segundo as suas familias, foram: d'Imna, a familia dos imnaitas: d'Isvi, a familia dos isvitas, de Berish, a familia dos beriitas.
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
Dos filhos de Beriah, foram; de Heber, a familia dos heberitas; de Malchiel, a familia dos malchielitas.
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
E o nome da filha d'Aser foi Serah.
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
Estas são as familias dos filhos d'Aser, segundo os que foram d'elles contados, cincoenta e tres mil e quatrocentos.
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
Os filhos de Naphtali, segundo as suas familias: de Jahzeel, a familia dos jahzeelitas: de Guni, a familia dos gunitas:
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
De Jezer, a familia dos jezeritas: de Sillem, a familia dos sillemitas.
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
Estas são as familias de Naphtali, segundo as suas familias: e os que foram d'elles contados, foram quarenta e cinco mil e quatrocentos.
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
Estes são os contados dos filhos d'Israel, seiscentos e um mil e setecentos e trinta.
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
E fallou o Senhor a Moysés, dizendo:
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
A estes se repartirá a terra em herança, segundo o numero dos nomes.
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
Aos muitos multiplicarás a sua herança, e aos poucos diminuirás a sua herança: a cada qual se dará a sua herança, segundo os que foram d'elles contados.
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
Todavia a terra se repartirá por sortes: segundo os nomes das tribus de seus paes a herdarão.
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
Segundo sair a sorte, se repartirá a herança d'elles entre os muitos e poucos.
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
E estes são os que foram contados de Levi, segundo as suas familias: de Gerson, a familia dos gersonitas; de Kohath, a familia dos kohathitas; de Merari, a familia dos meraritas.
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
Estas são as familias de Levi: a familia dos libnitas, a familia dos hebronitas, a familia dos mahlitas, a familia dos musitas, a familia dos corhitas: e Kohath gerou a Amram.
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
E o nome da mulher de Amram foi Jochebed, filha de Levi, a qual a Levi nasceu no Egypto: e esta a Amram pariu Aarão, e Moysés, e Miriam, sua irmã.
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
E a Aarão nasceram Nadab, Abihu, Eleazar, e Ithamar.
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
Porém Nadab e Abihu morreram quando trouxeram fogo estranho perante o Senhor.
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
E foram os que foram d'elles contados vinte e tres mil, todo o macho da edade de um mez e para cima: porque estes não foram contados entre os filhos de Israel, porquanto lhes não foi dada herança entre os filhos de Israel.
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
Estes são os que foram contados por Moysés e Eleazar, o sacerdote, que contaram os filhos de Israel nas campinas de Moab, ao pé do Jordão de Jericó.
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
E entre estes nenhum houve dos que foram contados por Moysés e Aarão, o sacerdote; quando contaram aos filhos de Israel no deserto de Sinai.
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
Porque o Senhor dissera d'elles que certamente morreriam no deserto: e nenhum d'elles ficou, senão Caleb, filho de Jefoné, e Josué, filho de Nun.

< Ƙidaya 26 >