< Ƙidaya 26 >

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
疫病の後、主はモーセと祭司アロンの子エレアザルとに言われた、
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
「イスラエルの人々の全会衆の総数をその父祖の家にしたがって調べ、イスラエルにおいて、すべて戦争に出ることのできる二十歳以上の者を数えなさい」。
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
そこでモーセと祭司エレアザルとは、エリコに近いヨルダンのほとりにあるモアブの平野で彼らに言った、
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
「主がモーセに命じられたように、あなたがたのうちの二十歳以上の者を数えなさい」。エジプトの地から出てきたイスラエルの人々は次のとおりである。
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
ルベンはイスラエルの長子である。ルベンの子孫は、ヘノクからヘノクびとの氏族が出、パルからパルびとの氏族が出、
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
ヘヅロンからヘヅロンびとの氏族が出、カルミからカルミびとの氏族が出た。
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
これらはルベンびとの氏族であって、数えられた者は四万三千七百三十人であった。
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
またパルの子はエリアブ。
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
エリアブの子はネムエル、ダタン、アビラムである。このダタンとアビラムとは会衆のうちから選び出された者で、コラのともがらと共にモーセとアロンとに逆らって主と争った時、
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
地は口を開いて彼らとコラとをのみ、その仲間は死んだ。その時二百五十人が火に焼き滅ぼされて、戒めの鏡となった。
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
ただし、コラの子たちは死ななかった。
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
シメオンの子孫は、その氏族によれば、ネムエルからネムエルびとの氏族が出、ヤミンからヤミンびとの氏族が出、ヤキンからヤキンびとの氏族が出、
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
ゼラからゼラびとの氏族が出、シャウルからシャウルびとの氏族が出た。
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
これらはシメオンびとの氏族であって、数えられた者は二万二千二百人であった。
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
ガドの子孫は、その氏族によれば、ゼポンからゼポンびとの氏族が出、ハギからハギびとの氏族が出、シュニからシュニびとの氏族が出、
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
オズニからオズニびとの氏族が出、エリからエリびとの氏族が出、
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
アロドからアロドびとの氏族が出、アレリからアレリびとの氏族が出た。
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
これらはガドの子孫の氏族であって、数えられた者は四万五百人であった。
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
ユダの子らはエルとオナンとであって、エルとオナンとはカナンの地で死んだ。
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
ユダの子孫は、その氏族によれば、シラからシラびとの氏族が出、ペレヅからペレヅびとの氏族が出、ゼラからゼラびとの氏族が出た。
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
ペレヅの子孫は、ヘヅロンからヘヅロンびとの氏族が出、ハムルからハムルびとの氏族が出た。
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
これらはユダの氏族であって、数えられた者は七万六千五百人であった。
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
イッサカルの子孫は、その氏族によれば、トラからトラびとの氏族が出、プワからプワびとの氏族が出、
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
ヤシュブからヤシュブびとの氏族が出、シムロンからシムロンびとの氏族が出た。
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
これらはイッサカルの氏族であって、数えられた者は六万四千三百人であった。
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
ゼブルンの子孫は、その氏族によれば、セレデからセレデびとの氏族が出、エロンからエロンびとの氏族が出、ヤリエルからヤリエルびとの氏族が出た。
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
これらはゼブルンびとの氏族であって、数えられた者は六万五百人であった。
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
ヨセフの子らは、その氏族によれば、マナセとエフライムとであって、
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
マナセの子孫は、マキルからマキルびとの氏族が出た。マキルからギレアデが生れ、ギレアデからギレアデびとの氏族が出た。
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
ギレアデの子孫は次のとおりである。イエゼルからイエゼルびとの氏族が出、ヘレクからヘレクびとの氏族が出、
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
アスリエルからアスリエルびとの氏族が出、シケムからシケムびとの氏族が出、
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
セミダからセミダびとの氏族が出、ヘペルからヘペルびとの氏族が出た。
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
ヘペルの子ゼロペハデには男の子がなく、ただ女の子のみで、ゼロペハデの女の子の名はマアラ、ノア、ホグラ、ミルカ、テルザといった。
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
これらはマナセの氏族であって、数えられた者は五万二千七百人であった。
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
エフライムの子孫は、その氏族によれば、次のとおりである。シュテラからはシュテラびとの氏族が出、ベケルからベケルびとの氏族が出、タハンからタハンびとの氏族が出た。
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
またシュテラの子孫は次のとおりである。すなわちエランからエランびとの氏族が出た。
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
これらはエフライムの子孫の氏族であって、数えられた者は三万二千五百人であった。以上はヨセフの子孫で、その氏族によるものである。
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
ベニヤミンの子孫は、その氏族によれば、ベラからベラびとの氏族が出、アシベルからアシベルびとの氏族が出、アヒラムからアヒラムびとの氏族が出、
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
シュパムからシュパムびとの氏族が出、ホパムからホパムびとの氏族が出た。
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
ベラの子はアルデとナアマンとであって、アルデからアルデびとの氏族が出、ナアマンからナアマンびとの氏族が出た。
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
これらはベニヤミンの子孫であって、その氏族によれば数えられた者は四万五千六百人であった。
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
ダンの子孫は、その氏族によれば、次のとおりである。シュハムからシュハムびとの氏族が出た。これらはダンの氏族であって、その氏族によるものである。
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
シュハムびとのすべての氏族のうち、数えられた者は六万四千四百人であった。
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
アセルの子孫は、その氏族によれば、エムナからエムナびとの氏族が出、エスイからエスイびとの氏族が出、ベリアからベリアびとの氏族が出た。
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
ベリアの子孫のうちヘベルからヘベルびとの氏族が出、マルキエルからマルキエルびとの氏族が出た。
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
アセルの娘の名はサラといった。
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
これらはアセルの子孫の氏族であって、数えられた者は五万三千四百人であった。
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
ナフタリの子孫は、その氏族によれば、ヤジエルからヤジエルびとの氏族が出、グニからグニびとの氏族が出、
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
エゼルからエゼルびとの氏族が出、シレムからシレムびとの氏族が出た。
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
これらはナフタリの氏族であって、その氏族により、数えられた者は四万五千四百人であった。
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
これらはイスラエルの子孫の数えられた者であって、六十万一千百三十人であった。
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
主はモーセに言われた、
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
「これらの人々に、その名の数にしたがって地を分け与え、嗣業とさせなさい。
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
大きい部族には多くの嗣業を与え、小さい部族には少しの嗣業を与えなさい。すなわち数えられた数にしたがって、おのおのの部族にその嗣業を与えなければならない。
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
ただし地は、くじをもって分け、その父祖の部族の名にしたがって、それを継がなければならない。
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
すなわち、くじをもってその嗣業を大きいものと、小さいものとに分けなければならない」。
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
レビびとのその氏族にしたがって数えられた者は次のとおりである。ゲルションからゲルションびとの氏族が出、コハテからコハテびとの氏族が出、メラリからメラリびとの氏族が出た。
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
レビの氏族は次のとおりである。すなわちリブニびとの氏族、ヘブロンびとの氏族、マヘリびとの氏族、ムシびとの氏族、コラびとの氏族であって、コハテからアムラムが生れた。
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
アムラムの妻の名はヨケベデといって、レビの娘である。彼女はエジプトでレビに生れた者であるが、アムラムにとついで、アロンとモーセおよびその姉妹ミリアムを産んだ。
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
アロンにはナダブ、アビウ、エレアザルおよびイタマルが生れた。
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
ナダブとアビウは異火を主の前にささげた時に死んだ。
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
その数えられた一か月以上のすべての男子は二万三千人であった。彼らはイスラエルの人々のうちに嗣業を与えられなかったため、イスラエルの人々のうちに数えられなかった者である。
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
これらはモーセと祭司エレアザルが、エリコに近いヨルダンのほとりにあるモアブの平野で数えたイスラエルの人々の数である。
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
ただしそのうちには、モーセと祭司アロンがシナイの荒野でイスラエルの人々を数えた時に数えられた者はひとりもなかった。
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
それは主がかつて彼らについて「彼らは必ず荒野で死ぬであろう」と言われたからである。それで彼らのうちエフンネの子カレブとヌンの子ヨシュアのほか、ひとりも残った者はなかった。

< Ƙidaya 26 >