< Ƙidaya 26 >

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
Après que le sang des coupables eut été répandu, le Seigneur dit à Moïse et à Eléazar, le prêtre, fils d’Aaron:
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
Faites le dénombrement complet des enfants d’Israël depuis vingt ans et au-dessus, selon leurs maisons et leur parenté, de tous ceux qui peuvent aller aux combats.
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
C’est pourquoi Moïse et Eléazar, le prêtre, parlèrent, dans les plaines de Moab, sur le Jourdain, contre Jéricho, à ceux qui avaient
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
Vingt ans et au-dessus, comme le Seigneur avait commandé, et dont voici le nombre:
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
Ruben, premier-né d’Israël; son fils Hénoch, de qui vient la famille des Hénochites; Phallu, de qui vient la famille des Phalluites;
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
Hesron, de qui vient la famille des Hesronites; et Charmi, de qui vient la famille des Charmites.
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
Telles sont les familles de la race de Ruben, dont le nombre trouvé fut de quarante-trois mille et sept cent trente.
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
Le fils de Phallu, fut Eliab;
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
Les fils de celui-ci, Namuel, Dathan et Abiron. Ce sont Dathan et Abiron, les princes du peuple, qui s’élevèrent contre Moïse et Aaron, dans la sédition de Coré, quand ils se révoltèrent contre le Seigneur,
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
Et que la terre, ouvrant sa bouche, dévora Coré, un grand nombre, étant morts; quand le feu brûla deux cent cinquante hommes. Alors il se fit un grand miracle,
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
Tel que, Coré périssant, ses fils ne périrent pas.
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
Les fils de Siméon selon leurs familles: Namuel; de lui vient la famille des Namuélites: Jamin; de lui vient la famille des Jaminites: Jachin; de lui vient la famille des Jachinites:
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
Zaré; de lui vient la famille des Zaréites: Saül; de lui vient la famille des Saülites.
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
Ce sont là les familles de la race de Siméon, dont le nombre total fut de vingt-deux mille deux cents.
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
Les fils de Gad, selon leur parenté: Séphon; de lui vient la famille des Séphonites: Aggi; de lui vient la famille des Aggites: Suni; de lui vient la famille des Sunites:
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
Ozni; de lui vient la famille des Oznites: Her; de lui vient la famille des Hérites:
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
Arod; de lui vient la famille des Arodites: Ariel; de lui vient la famille des Ariélites:
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
Telles sont les familles de Gad, dont le nombre total fut de quarante mille cinq cents.
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
Les fils de Juda: Her et Onan, qui tous deux moururent dans la terre de Chanaan.
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
Or, les fils de Juda furent, selon leur parenté: Séla, de qui vient la famille des Sélaïtes: Pharès, de qui vient la famille des Pharésites: Zaré, de qui vient la famille des Zaréites.
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
Mais les fils de Pharès: Hesron, de qui vient la famille des Hesronites; et Hamul, de qui vient la famille des Hamulites.
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
Telles sont les familles de Juda, dont le nombre total fut de soixante-seize mille cinq cents.
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
Les fils d’Issachar, selon leur parenté: Tola, de qui vient la famille des Tolaïtes: Phua, de qui vient la famille des Phuaïtes:
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
Jasub, de qui vient la famille des Jasubites: Semran, de qui vient la famille des Semranites.
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
Telle est la parenté d’Issachar, dont le nombre total fut de soixante-quatre mille trois cents.
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
Les fils de Zabulon, selon leur parenté: Sared, de qui vient la famille des Sarédites: Elon, de qui vient la famille des Elonites: Jalel, de qui vient la famille des Jalélites.
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
Telle est la parenté de Zabulon, dont le nombre fut de soixante mille cinq cents.
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
Les fils de Joseph, selon leur parenté: Manassé et Ephraïm.
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
De Manassé naquit Machir, de qui vient la famille des Machirites. Machir engendra Galaad, de qui vient la famille des Galaadites.
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
Galaad eut des fils: Jézer, de qui vient la famille des Jézérites: Hélec, de qui vient la famille des Hélécites:
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
Asriel, de qui vient la famille des Asriélites: Séchem, de qui vient la famille des Séchémites:
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
Sémida, de qui vient la famille des Sémidaïtes; et Hépher, de qui vient la famille des Héphérites.
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
Or Hépher fut père de Salphaad qui n’eut point de fils, mais seulement des filles, dont les noms sont: Maala, Noa, Hégla, Melcha et Thersa.
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
Ce sont là les familles de Manassé, et leur nombre fut de cinquante-deux mille sept cents.
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
Mais les enfants d’Ephraïm, selon leur parenté, furent ceux-ci: Suthala, de qui vient la famille des Suthalaïtes: Bécher, de qui vient la famille des Béchérites: Théhen, de qui vient la famille des Théhénites.
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
Or, le fils de Suthala fut Héran, de qui vient la famille des Héranites.
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
Telle est la parenté des fils d’Ephraïm, dont le nombre fut de trente-deux mille cinq cents.
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
Ce sont là les fils de Joseph, selon leurs familles. Les fils de Benjamin, selon leur parenté: Béla, de qui vient la famille des Bélaïtes: Asbel, de qui vient la famille des Asbélites: Ahiram, de qui vient la famille des Ahiramites.
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
Supham, de qui vient la famille des Suphamites: Hupham, de qui vient la famille des Huphamites.
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
Les fils de Béla: Héred et Noéman. De Héred vient la famille des Hérédites; de Noéman, la famille des Noémanites.
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
Ce sont là les fils de Benjamin, selon leur parenté, dont le nombre fut de quarante-cinq mille six cents.
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
Les fils de Dan, selon leur parenté: Suham, de qui vient la famille des Suhamites. Telle est la parenté de Dan, selon ses familles.
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
Tous furent Suhamites, dont le nombre était de soixante-quatre mille quatre cents.
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
Les fils d’Aser, selon leur parenté: Jemna, de qui vient la famille des Jemnaïtes: Jessui de qui vient la famille des Jessuites: Brié, de qui vient la famille des Briéites.
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
Les fils de Brié: Héber, de qui vient la famille des Hébérites. et Melchiel, de qui vient la famille des Melchiélites.
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
Mais le nom de la fille d’Aser fut Sara.
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
Telle est la parenté des fils d’Aser, et leur nombre fut de cinquante-trois mille quatre cents.
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
Les fils de Nephthali, selon leur parenté: Jésiel, de qui vient la famille des Jésiélites: Guni, de qui vient la famille des Gunites.
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
Jéser, de qui vient la famille des Jésérites: Sellem, de qui vient la famille des Sellémites.
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
Telle est la parenté des fils de Nephthali, selon leurs familles, et dont le nombre fut de quarante-cinq mille quatre cents.
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
C’est là le nombre des enfants d’Israël qui furent recensés: six cent et un mille sept cent trente.
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla ensuite à Moïse, disant:
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
La terre leur sera partagée selon le nombre des noms, pour être leurs possessions.
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
Au plus grand nombre tu donneras la plus grande partie, et au plus petit nombre, la moindre; à chacun sera remise sa possession, selon qu’il vient d’être recensé;
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
De manière seulement que ce soit le sort qui partage la terre aux tribus et aux familles.
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
Tout ce qui sera échu par le sort, c’est ce que recevra ou le plus grand nombre ou le plus petit nombre.
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
Voici aussi le nombre des fils de Lévi, selon leurs familles: Gerson, de qui vient la famille des Gersonites: Caath, de qui vient la famille des Caathites: Mérari, de qui vient la famille des Mérarites.
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
Voici les familles de Lévi: la famille de Lobni, la famille d’Hébroni, la famille de Moholi, la famille de Musi, la famille de Coré.
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
Qui eut pour femme Jochabed, fille de Lévi, laquelle naquit en Egypte; c’est elle qui engendra à Amram, son mari, ses fils, Aaron et Moïse, et Marie leur sœur.
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
D’Aaron naquirent: Nadab, Abiu, Eléazar, et Ithamar;
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
Dont Nadab et Abiu moururent, lorsqu’ils eurent offert un feu étranger devant le Seigneur.
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
Ainsi tous ceux qui furent dénombrés, s’élevèrent à vingt-trois mille du sexe masculin, depuis un mois et au-dessus, parce qu’ils ne furent pas recensés parmi les enfants d’Israël, et qu’il ne leur fut pas donné de possession avec les autres.
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
C’est là le nombre des enfants d’Israël, qui furent enregistrés par Moïse et Eléazar, le prêtre, dans les plaines de Moab, sur le Jourdain, contre Jéricho;
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
Parmi lesquels il ne s’en trouva aucun de ceux qui avaient été dénombrés auparavant par Moïse et Aaron dans le désert de Sinaï.
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
Carie Seigneur avait prédit que tous mourraient dans le désert. Ainsi, il ne resta pas un seul d’eux, si ce n’est Caleb, fils de Jéphoné, et Josué, fils de Nun.

< Ƙidaya 26 >