< Ƙidaya 26 >
1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
Et après ce fléau l'Éternel parla à Moïse et à Eléazar, fils du Prêtre Aaron, en ces termes:
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
Faites le relevé de la totalité de l'Assemblée des enfants d'Israël, des hommes âgés de vingt ans et plus, selon leurs maisons patriarcales, de tous ceux qui font le service militaire en Israël.
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
Et Moïse et le Prêtre Eléazar leur parlèrent dans les plaines de Moab sur le Jourdain près de Jéricho, et dirent:
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
De vingt ans et au-dessus, comme l'Éternel l'a prescrit à Moïse, et aux enfants d'Israël sortis du pays d'Egypte:
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
Ruben, premier-né d'Israël, fils de Ruben: Hanoch, famille des Hanochites; de Pallu, la famille des Palluites;
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
de Hestron, la famille des Hestronites; de Carmi, la famille des Carmites.
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
Telles sont les familles, des Rubénites, dont quarante-trois mille sept cent trente furent enregistrés.
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
Et le fils de Pallu était Eliab;
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
et les fils d'Eliab, Nemuel et Dathan et Abiram. C'est ce Dathan et cet Abiram, députés de l'Assemblée, qui, dans l'attroupement de Coré, se soulevèrent contre Moïse et Aaron, lors de leur soulèvement contre l'Éternel,
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
quand la terre s'entr'ouvrant les engloutit eux et Coré, en même temps que périssait cette troupe, le feu ayant consumé les deux cent cinquante hommes dont il fut fait un exemple.
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
Cependant les fils de Coré ne périrent pas.
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
Fils de Siméon, selon leurs familles: de Nemuel, la famille des Nemuélites; de Jamin, la famille des Jaminites; de Jachin, la famille des Jachinites;
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
de Zérah, la famille des Zérahites; de Saul, la famille des Saulites.
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
Telles sont les familles des Siméonites: vingt-deux mille deux cents.
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
Fils de Gad selon leurs familles: de Tsephon, la famille des Tsephonites; de Haggi, la famille des Haggites: de Suni, la famille des Sunites;
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
de Ozéni, la famille des Ozénites; de Eri la famille des Erites;
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
de Arod, la famille des Arodites; de Areli, la famille des Arelites.
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
Telles sont les familles des fils de Gad dont quarante mille cinq cents furent enregistrés.
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
Fils de Juda: Er et Onan; mais Er et Onan étaient morts dans le pays de Canaan.
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
Et les fils de Juda étaient d'après leurs familles: de Séla, la famille des Sélanites; de Pérets, la famille des Péretsites; de Zerah, la famille des Zerahites.
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
Et les fils de Pérets furent: de Hetsron, la famille des Hetsronites; de Hamul, la famille des Hamulites.
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
Telles sont les familles de Juda: soixante-seize mille cinq cents furent enregistrés.
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
Fils d'Issaschar, selon leurs familles: de Thola, la famille des Tholaïtes; de Puva, la famille des Punites;
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
de Jasub, la famille des Jasubites; de Simron, la famille des Simronites.
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
telles sont les familles d'Issaschar: soixante-quatre mille trois cents furent enregistrés.
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
Fils de Zabulon, selon leurs familles: de Sered, la famille des Sardites; de Elon, la famille des Elonites; de Jahléel, la famille des Jahléélites.
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
Telles sont les familles des Zabulonites dont soixante mille cinq cents furent enregistrés.
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
Fils de Joseph selon leurs familles: Manassé et Ephraïm.
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
Fils de Manassé: de Machir, la famille des Machirites (et Machir engendra Galaad); de Galaad, la famille des Galaadites.
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
Voici les fils de Galaad: Hiézer, la famille des Hiézérites; de Hélek, la famille des Hélékites;
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
et Asriel, la famille des Asriélites; et Sichem, la famille des Sichémites;
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
et Semidah, la famille des Semidahites; et Hépher, la famille des Héphrites.
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
Et Tselophehad était fils de Hépher, il n'avait point de fils, seulement des filles; et les noms des filles de Tselophehad étaient: Mahela et Noa, Hogla, Milca et Thirtsa.
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
Telles sont les familles de Manassé: cinquante-deux mille sept cents furent enregistrés.
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
Suivent les fils d'Epbraïm, selon leurs familles: de Suthélah, la famille des Suthélahites; de Becher, la famille des Bachrites; de Thahan, la famille des Thahanites.
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
Et voici les fils de Suthélah: de Eran, la famille des Eranites.
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
Telles sont les familles des fils d'Éphraïm dont trente-deux mille cinq cents furent enregistrés. Tels sont les fils de Joseph selon leurs familles.
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
Fils de Benjamin, selon leurs familles: de Béla, la famille des Balites; de Asbel, la famille des Asbélites; de Ahiram, la famille des Ahiramites;
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
de Sephupham, la famille des Suphamites; de Hupham, la famille des Huphamites.
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
Et les fils de Béla furent: Ard et Naëman, la famille des Ardites; de Naëman, la famille des Naëmanites.
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
Tels sont les fils de Benjamin selon leurs familles: quarante-cinq mille six cents furent enregistrés.
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
Voici les fils de Dan, selon leurs familles: de Suham, la famille des Suhamites; telles sont les familles de Dan selon leurs familles.
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
Toutes les familles des Suhamites fournirent soixante-quatre mille quatre cents hommes enregistrés.
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
Fils d'Asser, selon leurs familles: de Jimna, la famille des Jimnaïtes; de Jisvi, la famille des Jïsvites; de Béria, la famille des Bériites.
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
Des fils de Béria: de Héber, la famille des Hébrites; de Malchiel, la famille dés Malchiélites.
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
Et le nom de la fille d'Asser était Sarah.
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
Telles sont les familles des fils d'Asser dont cinquante-trois mille quatre cents furent enregistrés.
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
Fils de Nephthali, selon leurs familles: de Jahtsehl, la famille des Jahtsehlites; de Guni, la famille des Gunites;
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
de Jetser, la famille des Jetsérites; de Sillem, la famille des Sillémites.
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
Telles sont les familles de Nephthali selon leurs familles: quarante-cinq mille quatre cents hommes furent enregistrés.
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
Tels sont les hommes des enfants d'Israël enregistrés au nombre de six cent un mille sept cent trente.
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l'Éternel parla à Moïse en ces termes:
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
C'est entre eux que sera partagé le pays en autant de propriétés qu'il y a de noms:
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
aux plus nombreux tu adjugeras un lot plus grand et un plus petit aux moins nombreux; il sera donné à chacun un héritage proportionné au nombre de ses hommes enregistrés.
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
Cependant le partage du pays se fera au sort; les propriétés seront affectées aux noms de leurs tribus patriarcales;
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
c'est par le sort qu'à chacun sera adjugé son lot, plus ou moins considérable.
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
Et voici les Lévites enregistrés selon leurs familles: de Gerson, la famille des Gersonites; de Kahath, la famille des Kahathites;
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
de Merari, la famille des Merarites. Voici les familles de Lévi: la famille des Libnites, la famille des Hébronites, la famille des Mahelites, la famille des Musites, la famille des Corahites. Et Kahath engendra Amram.
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
Et le nom de la femme d'Amram était Jochébed, fille de Lévi, laquelle naquit à Lévi en Egypte; et elle enfanta à Amram Aaron et Moïse et Marie, leur sœur.
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
Et à Aaron naquirent Nadab et Abihu, Eléazar et Ithamar.
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
Et Nadab et Abihu moururent lorsqu'ils présentèrent devant l'Éternel un feu étranger.
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
Et leurs hommes enregistrés étaient au nombre de vingt-trois mille, tous mâles, d'un mois et au-dessus; car ils ne furent pas compris dans le recensement des enfants d'Israël, parce qu'il ne leur fut adjugé aucune propriété parmi les enfants d'Israël.
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
Tels sont les hommes recensés par Moïse et le Prêtre Eléazar qui recensèrent les enfants d'Israël dans les plaines de Moab sur le Jourdain de Jéricho.
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
Et parmi eux il ne se trouvait plus aucun des hommes recensés par Moïse et le Prêtre Aaron, lors du recensement fait des enfants d'Israël dans le désert de Sinaï.
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
Car l'Éternel avait, dit d'eux: Ils mourront, mourront dans le désert, et il n'en survivra pas un, sinon Caleb, fils de Jephunné, et Josué, fils de Nun.