< Ƙidaya 26 >

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
And it came to pass after the plague, that YHWH spake unto Moses and unto Eleazar the son of Aaron the priest, saying,
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
Take the sum of all the congregation of the children of Israel, from twenty years old and upward, throughout their father's house, all that are able to go to war in Israel.
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
And Moses and Eleazar the priest spake with them in the plains of Moab by Jordan near Jericho, saying,
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
Take the sum of the people, from twenty years old and upward; as YHWH commanded Moses and the children of Israel, which went forth out of the land of Egypt.
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
Reuben, the eldest son of Israel: the children of Reuben; Hanoch, of whom cometh the family of the Hanochites: of Pallu, the family of the Palluites:
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
Of Hezron, the family of the Hezronites: of Carmi, the family of the Carmites.
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
These are the families of the Reubenites: and they that were numbered of them were forty and three thousand and seven hundred and thirty.
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
And the sons of Pallu; Eliab.
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
And the sons of Eliab; Nemuel, and Dathan, and Abiram. This is that Dathan and Abiram, which were famous in the congregation, who strove against Moses and against Aaron in the company of Korah, when they strove against YHWH:
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
And the earth opened her mouth, and swallowed them up together with Korah, when that company died, what time the fire devoured two hundred and fifty men: and they became a sign.
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
Notwithstanding the children of Korah died not.
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
The sons of Simeon after their families: of Nemuel, the family of the Nemuelites: of Jamin, the family of the Jaminites: of Jachin, the family of the Jachinites:
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
Of Zerah, the family of the Zarhites: of Shaul, the family of the Shaulites.
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
These are the families of the Simeonites, twenty and two thousand and two hundred.
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
The children of Gad after their families: of Zephon, the family of the Zephonites: of Haggi, the family of the Haggites: of Shuni, the family of the Shunites:
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
Of Ozni, the family of the Oznites: of Eri, the family of the Erites:
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
Of Arod, the family of the Arodites: of Areli, the family of the Arelites.
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
These are the families of the children of Gad according to those that were numbered of them, forty thousand and five hundred.
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
The sons of Judah were Er and Onan: and Er and Onan died in the land of Canaan.
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
And the sons of Judah after their families were; of Shelah, the family of the Shelanites: of Pharez, the family of the Pharzites: of Zerah, the family of the Zarhites.
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
And the sons of Pharez were; of Hezron, the family of the Hezronites: of Hamul, the family of the Hamulites.
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
These are the families of Judah according to those that were numbered of them, threescore and sixteen thousand and five hundred.
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
Of the sons of Issachar after their families: of Tola, the family of the Tolaites: of Pua, the family of the Punites:
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
Of Jashub, the family of the Jashubites: of Shimron, the family of the Shimronites.
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
These are the families of Issachar according to those that were numbered of them, threescore and four thousand and three hundred.
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
Of the sons of Zebulun after their families: of Sered, the family of the Sardites: of Elon, the family of the Elonites: of Jahleel, the family of the Jahleelites.
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
These are the families of the Zebulunites according to those that were numbered of them, threescore thousand and five hundred.
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
The sons of Joseph after their families were Manasseh and Ephraim.
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
Of the sons of Manasseh: of Machir, the family of the Machirites: and Machir begat Gilead: of Gilead come the family of the Gileadites.
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
These are the sons of Gilead: of Jeezer, the family of the Jeezerites: of Helek, the family of the Helekites:
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
And of Asriel, the family of the Asrielites: and of Shechem, the family of the Shechemites:
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
And of Shemida, the family of the Shemidaites: and of Hepher, the family of the Hepherites.
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
And Zelophehad the son of Hepher had no sons, but daughters: and the names of the daughters of Zelophehad were Mahlah, and Noah, Hoglah, Milcah, and Tirzah.
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
These are the families of Manasseh, and those that were numbered of them, fifty and two thousand and seven hundred.
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
These are the sons of Ephraim after their families: of Shuthelah, the family of the Shuthalhites: of Becher, the family of the Bachrites: of Tahan, the family of the Tahanites.
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
And these are the sons of Shuthelah: of Eran, the family of the Eranites.
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
These are the families of the sons of Ephraim according to those that were numbered of them, thirty and two thousand and five hundred. These are the sons of Joseph after their families.
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
The sons of Benjamin after their families: of Bela, the family of the Belaites: of Ashbel, the family of the Ashbelites: of Ahiram, the family of the Ahiramites:
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
Of Shupham, the family of the Shuphamites: of Hupham, the family of the Huphamites.
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
And the sons of Bela were Ard and Naaman: of Ard, the family of the Ardites: and of Naaman, the family of the Naamites.
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
These are the sons of Benjamin after their families: and they that were numbered of them were forty and five thousand and six hundred.
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
These are the sons of Dan after their families: of Shuham, the family of the Shuhamites. These are the families of Dan after their families.
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
All the families of the Shuhamites, according to those that were numbered of them, were threescore and four thousand and four hundred.
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
Of the children of Asher after their families: of Jimna, the family of the Jimnites: of Jesui, the family of the Jesuites: of Beriah, the family of the Beriites.
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
Of the sons of Beriah: of Heber, the family of the Heberites: of Malchiel, the family of the Malchielites.
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
And the name of the daughter of Asher was Sarah.
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
These are the families of the sons of Asher according to those that were numbered of them; who were fifty and three thousand and four hundred.
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
Of the sons of Naphtali after their families: of Jahzeel, the family of the Jahzeelites: of Guni, the family of the Gunites:
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
Of Jezer, the family of the Jezerites: of Shillem, the family of the Shillemites.
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
These are the families of Naphtali according to their families: and they that were numbered of them were forty and five thousand and four hundred.
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
These were the numbered of the children of Israel, six hundred thousand and a thousand seven hundred and thirty.
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH spake unto Moses, saying,
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
Unto these the land shall be divided for an inheritance according to the number of names.
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
To many thou shalt give the more inheritance, and to few thou shalt give the less inheritance: to every one shall his inheritance be given according to those that were numbered of him.
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
Notwithstanding the land shall be divided by lot: according to the names of the tribes of their fathers they shall inherit.
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
According to the lot shall the possession thereof be divided between many and few.
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
And these are they that were numbered of the Levites after their families: of Gershon, the family of the Gershonites: of Kohath, the family of the Kohathites: of Merari, the family of the Merarites.
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
These are the families of the Levites: the family of the Libnites, the family of the Hebronites, the family of the Mahlites, the family of the Mushites, the family of the Korathites. And Kohath begat Amram.
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
And the name of Amram's wife was Jochebed, the daughter of Levi, whom her mother bare to Levi in Egypt: and she bare unto Amram Aaron and Moses, and Miriam their sister.
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
And unto Aaron was born Nadab, and Abihu, Eleazar, and Ithamar.
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
And Nadab and Abihu died, when they offered strange fire before YHWH.
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
And those that were numbered of them were twenty and three thousand, all males from a month old and upward: for they were not numbered among the children of Israel, because there was no inheritance given them among the children of Israel.
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
These are they that were numbered by Moses and Eleazar the priest, who numbered the children of Israel in the plains of Moab by Jordan near Jericho.
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
But among these there was not a man of them whom Moses and Aaron the priest numbered, when they numbered the children of Israel in the wilderness of Sinai.
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
For YHWH had said of them, They shall surely die in the wilderness. And there was not left a man of them, save Caleb the son of Jephunneh, and Joshua the son of Nun.

< Ƙidaya 26 >