< Ƙidaya 26 >

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
After the plague had ended, the LORD said to Moses and Eleazar son of Aaron the priest,
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
“Take a census of the whole congregation of Israel by the houses of their fathers—all those twenty years of age or older who can serve in the army of Israel.”
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
So on the plains of Moab by the Jordan, across from Jericho, Moses and Eleazar the priest issued the instruction,
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
“Take a census of the men twenty years of age or older, as the LORD has commanded Moses.” And these were the Israelites who came out of the land of Egypt:
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
Reuben was the firstborn of Israel. These were the descendants of Reuben: The Hanochite clan from Hanoch, the Palluite clan from Pallu,
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
the Hezronite clan from Hezron, and the Carmite clan from Carmi.
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
These were the clans of Reuben, and their registration numbered 43,730.
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
Now the son of Pallu was Eliab,
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
and the sons of Eliab were Nemuel, Dathan, and Abiram. It was Dathan and Abiram, chosen by the congregation, who fought against Moses and Aaron with the followers of Korah who rebelled against the LORD.
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
And the earth opened its mouth and swallowed them along with Korah, whose followers died when the fire consumed 250 men. They serve as a warning sign.
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
However, the line of Korah did not die out.
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
These were the descendants of Simeon by their clans: The Nemuelite clan from Nemuel, the Jaminite clan from Jamin, the Jachinite clan from Jachin,
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
the Zerahite clan from Zerah, and the Shaulite clan from Shaul.
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
These were the clans of Simeon, and there were 22,200 men.
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
These were the descendants of Gad by their clans: The Zephonite clan from Zephon, the Haggite clan from Haggi, the Shunite clan from Shuni,
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
the Oznite clan from Ozni, the Erite clan from Eri,
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
the Arodite clan from Arod, and the Arelite clan from Areli.
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
These were the clans of Gad, and their registration numbered 40,500.
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
The sons of Judah were Er and Onan, but they died in the land of Canaan.
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
These were the descendants of Judah by their clans: The Shelanite clan from Shelah, the Perezite clan from Perez, and the Zerahite clan from Zerah.
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
And these were the descendants of Perez: the Hezronite clan from Hezron and the Hamulite clan from Hamul.
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
These were the clans of Judah, and their registration numbered 76,500.
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
These were the descendants of Issachar by their clans: The Tolaite clan from Tola, the Punite clan from Puvah,
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
the Jashubite clan from Jashub, and the Shimronite clan from Shimron.
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
These were the clans of Issachar, and their registration numbered 64,300.
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
These were the descendants of Zebulun by their clans: The Seredite clan from Sered, the Elonite clan from Elon, and the Jahleelite clan from Jahleel.
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
These were the clans of Zebulun, and their registration numbered 60,500.
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
The descendants of Joseph included the clans of Manasseh and Ephraim.
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
These were the descendants of Manasseh: The Machirite clan from Machir, the father of Gilead, and the Gileadite clan from Gilead.
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
These were the descendants of Gilead: the Iezerite clan from Iezer, the Helekite clan from Helek,
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
the Asrielite clan from Asriel, the Shechemite clan from Shechem,
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
the Shemidaite clan from Shemida, and the Hepherite clan from Hepher.
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
Now Zelophehad son of Hepher had no sons but only daughters. The names of his daughters were Mahlah, Noah, Hoglah, Milcah, and Tirzah.
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
These were the clans of Manasseh, and their registration numbered 52,700.
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
These were the descendants of Ephraim by their clans: The Shuthelahite clan from Shuthelah, the Becherite clan from Becher, and the Tahanite clan from Tahan.
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
And the descendants of Shuthelah were the Eranite clan from Eran.
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
These were the clans of Ephraim, and their registration numbered 32,500. These clans were the descendants of Joseph.
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
These were the descendants of Benjamin by their clans: The Belaite clan from Bela, the Ashbelite clan from Ashbel, the Ahiramite clan from Ahiram,
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
the Shuphamite clan from Shupham, and the Huphamite clan from Hupham.
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
And the descendants of Bela from Ard and Naaman were the Ardite clan from Ard and the Naamite clan from Naaman.
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
These were the clans of Benjamin, and their registration numbered 45,600.
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
These were the descendants of Dan by their clans: The Shuhamite clan from Shuham. These were the clans of Dan.
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
All of them were Shuhamite clans, and their registration numbered 64,400.
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
These were the descendants of Asher by their clans: The Imnite clan from Imnah, the Ishvite clan from Ishvi, and the Beriite clan from Beriah.
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
And these were the descendants of Beriah: the Heberite clan from Heber and the Malchielite clan from Malchiel.
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
And the name of Asher’s daughter was Serah.
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
These were the clans of Asher, and their registration numbered 53,400.
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
These were the descendants of Naphtali by their clans: The Jahzeelite clan from Jahzeel, the Gunite clan from Guni,
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
the Jezerite clan from Jezer, and the Shillemite clan from Shillem.
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
These were the clans of Naphtali, and their registration numbered 45,400.
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
These men of Israel numbered 601,730 in all.
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then the LORD said to Moses,
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
“The land is to be divided among the tribes as an inheritance, according to the number of names.
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
Increase the inheritance for a large tribe and decrease it for a small one; each tribe is to receive its inheritance according to the number of those registered.
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
Indeed, the land must be divided by lot; they shall receive their inheritance according to the names of the tribes of their fathers.
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
Each inheritance is to be divided by lot among the larger and smaller tribes.”
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
Now these were the Levites numbered by their clans: The Gershonite clan from Gershon, the Kohathite clan from Kohath, and the Merarite clan from Merari.
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
These were the families of the Levites: The Libnite clan, the Hebronite clan, the Mahlite clan, the Mushite clan, and the Korahite clan. Now Kohath was the father of Amram,
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
and Amram’s wife was named Jochebed. She was also a daughter of Levi, born to Levi in Egypt. To Amram she bore Aaron, Moses, and their sister Miriam.
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
Nadab, Abihu, Eleazar, and Ithamar were born to Aaron,
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
but Nadab and Abihu died when they offered unauthorized fire before the LORD.
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
The registration of the Levites totaled 23,000, every male a month old or more; they were not numbered among the other Israelites, because no inheritance was given to them among the Israelites.
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
These were the ones numbered by Moses and Eleazar the priest when they counted the Israelites on the plains of Moab by the Jordan, across from Jericho.
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
Among all these, however, there was not one who had been numbered by Moses and Aaron the priest when they counted the Israelites in the Wilderness of Sinai.
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
For the LORD had told them that they would surely die in the wilderness. Not one was left except Caleb son of Jephunneh and Joshua son of Nun.

< Ƙidaya 26 >