< Ƙidaya 25 >
1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
Cuando los israelitas se alojaban en Sitím los hombres empezaron a tener sexo con mujeres moabitas
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
que los invitaban a los sacrificios hechos a sus dioses. Los israelitas comían las comidas paganas y se inclinaban ante estos dioses.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
De esta manera los israelitas se dedicaban a la adoración de Baal de Peor, y el Señor estaba enojado con ellos.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
El Señor le dijo a Moisés, “Arresta a todos los líderes israelitas y mátalos ante el Señor donde todos puedan ver para alejar la furiosa ira del Señor del pueblo”.
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
Así que Moisés instruyó a los jueces de Israel, “Cada uno de ustedes tiene que matar a todos sus hombres que se han dedicado a adorar a Baal de Peor”.
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
En ese momento un hombre israelita llevó a una mujer madianita a la tienda de su familia a la vista de Moisés y de todos los israelitas mientras lloraban a la entrada del Tabernáculo de Reunión.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
Al ver esto, Finees, hijo de Eleazar, hijo del sacerdote Aarón, abandonó la asamblea, agarró una lanza
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
y siguió al hombre a su tienda. Allí, Finees atravesó con la lanza a ambos, al israelita y al estómago de la mujer. Esta acción detuvo la plaga que había empezado a matar a los israelitas,
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
pero ya habían muerto 24.000.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
El Señor le dijo a Moisés,
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
“Finees hijo de Eleazar, hijo del sacerdote Aarón, ha alejado mi ira de los israelitas, porque de todos ellos estaba fervorosamente dedicado a mí, así que no destruí a los israelitas en mi apasionada ira.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
Así que anunciad que le concedo mi acuerdo de paz.
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
Será un acuerdo que asegura un sacerdocio permanente para él y sus descendientes, porque se dedicó apasionadamente a su Dios y enderezó a los israelitas”.
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
El nombre del israelita que fue asesinado con la mujer madianita era Zimri, hijo de Salu, un líder de la familia de la tribu de Simeón.
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
El nombre de la mujer madianita que fue asesinada era Cozbi, hija de Zur, un líder de familia de la tribu de Madián.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
El Señor le dijo a Moisés:
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
“Ataca a los madianitas y mátalos,
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
porque te atacaron engañosamente, llevándote por mal camino al usar a Peor y a su mujer Cozbi, la hija del líder madianita – la mujer que fue asesinada el día que llegó la plaga por su devoción a Peor –”.