< Ƙidaya 25 >
1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
И живяше Израиль в Саттиме, и осквернишася людие блужением со дщерми Моавли:
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
и призваша я в требы кумир своих, и ядоша людие требы их и поклонишася кумиром их:
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
и причастися Израиль Веельфегору, и разгневася яростию Господь на Израиля.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
И рече Господь к Моисею: поими вся князи людския, и обличи я Господу прямо солнцу, и отвратится гнев ярости Господни от Израиля.
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
И рече Моисей к племенем Израилским: избийте кийждо ужика своего служившаго Веельфегору.
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
И се, человек от сынов Израилевых пришед приведе брата своего к Мадианитыне пред Моисеем и пред всем сонмом Израилевым: сии же плакахуся пред дверми скинии свидения.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
И видев Финеес, сын Елеазара сына Аарона жерца, воста из среды сонма, и взем сулицу в руку,
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
вниде вслед человека Израилтянина в блудилище, и прободе обоих, и человека Израилтянина, и жену сквозе ложесна ея: и преста вред от сынов Израилевых.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
И быша умершии язвою двадесять четыри тысящы.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
И рече Господь к Моисею, глаголя:
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
Финеес сын Елеазара сына Аарона жерца утоли гнев Мой от сынов Израилевых, егда возревнова ревность Моя в них, и не потребих сынов Израилевых в ревности Моей:
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
тако рцы: се, Аз даю ему заветзавет Мой мирный,
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
и будет ему и семени его по нем завет жречества вечный, понеже возревнова по Бозе своем и умилостиви о сынех Израилевых.
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
Имя же человеку Израилтянину, егоже уби с Мадианитынею, Замврий сын Салмонь, князь дому отечества сынов Симеоних:
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
и имя жене Мадианитыне прободеной Хазви, дщи Сура, князя рода Соммофова, дому отечества есть Мадиамля.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
И рече Господь к Моисею, глаголя: рцы сыном Израилевым, глаголя:
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
враждуйте Мадианитом и бийте я:
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
зане враждуют вам сии лестию, елико прельщают вас Фогором и Хазвиею дщерию князя Мадиамля, сестрою своею прободеною, в день язвы Фогора ради.