< Ƙidaya 25 >

1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
Israel ficou em Shittim; e o povo começou a brincar de prostituta com as filhas de Moab;
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
pois elas chamaram o povo para os sacrifícios de seus deuses. O povo comeu e se curvou diante de seus deuses.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
Israel se uniu a Baal Peor, e a raiva de Javé ardeu contra Israel.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
Javé disse a Moisés: “Pegue todos os chefes do povo e pendure-os diante de Javé diante do sol, para que a raiva feroz de Javé se afaste de Israel”.
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
Moisés disse aos juízes de Israel: “Todos matam seus homens que se uniram a Baal Peor”.
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
Eis que um dos filhos de Israel veio e trouxe a seus irmãos uma mulher midianita aos olhos de Moisés e de toda a congregação dos filhos de Israel, enquanto choravam à porta da Tenda da Reunião.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
Quando Phinehas, o filho de Eleazar, o filho de Arão, o sacerdote, viu isso, levantou-se do meio da congregação e pegou uma lança em sua mão.
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
Ele foi atrás do homem de Israel até o pavilhão, e empurrou ambos, o homem de Israel, e a mulher através de seu corpo. Então a peste foi detida entre os filhos de Israel.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
Os que morreram pela peste eram vinte e quatro mil.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh falou a Moisés, dizendo:
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
“Phinehas, o filho de Eleazar, o filho de Arão, o sacerdote, afastou minha ira dos filhos de Israel, pois tinha ciúmes com meu ciúme entre eles, para que eu não consumisse os filhos de Israel em meu ciúme.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
Por isso diz: “Eis que eu lhe dou meu pacto de paz”.
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
Será para ele, e para seus descendentes depois dele, o pacto de um sacerdócio eterno, porque teve inveja de seu Deus, e fez expiação pelos filhos de Israel””.
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
Now o nome do homem de Israel que foi morto, que foi morto com a mulher midianita, era Zimri, o filho de Salu, príncipe da casa de um pai entre os simeonitas.
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
O nome da mulher midianita que foi assassinada era Cozbi, a filha de Zur. Ele era o chefe do povo da casa de um pai em Midian.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh falou a Moisés, dizendo:
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
“Ataquem os midianitas, e ataquem-nos;
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
pois eles o assediaram com suas artimanhas, em que o enganaram no caso de Peor, e no incidente relativo a Cozbi, a filha do príncipe de Midian, sua irmã, que foi assassinada no dia da praga no caso de Peor”.

< Ƙidaya 25 >