< Ƙidaya 25 >

1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
Alors Israël demeurait en Sittim, et le peuple commença à paillarder avec les filles de Moab.
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
Car elles convièrent le peuple aux sacrifices de leurs dieux, et le peuple y mangea, et se prosterna devant leurs dieux.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
Et Israël s'accoupla à Bahal-Péhor; c'est pourquoi la colère de l'Eternel s'enflamma contre Israël.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
Et l'Eternel dit à Moïse: Prends tous les chefs du peuple, et les fais pendre devant l'Eternel au soleil, et l'ardeur de la colère de l'Eternel se détournera d'Israël.
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
Moïse donc dit aux juges d'Israël: Que chacun de vous fasse mourir les hommes qui sont à sa charge, lesquels se sont joints à Bahal-Péhor.
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
Et voici, un homme des enfants d'Israël vint, et amena à ses frères une Madianite, devant Moïse et devant toute l'assemblée des enfants d'Israël, comme ils pleuraient à la porte du Tabernacle d'assignation.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
Ce que Phinées, fils d'Eléazar, fils d'Aaron le Sacrificateur ayant vu, il se leva du milieu de l'assemblée, et prit une javeline en sa main.
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
Et il entra vers l'homme Israélite dans la tente, et les transperça tous deux par le ventre, l'homme Israélite et la femme; et la plaie fut arrêtée de dessus les enfants d'Israël.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
Or il y en eut vingt-quatre mille qui moururent de cette plaie.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
Phinées, fils d'Eléazar, fils d'Aaron, le Sacrificateur, a détourné ma colère de dessus les enfants d'Israël, parce qu'il a été animé de mon zèle au milieu d'eux, et je n'ai point consumé les enfants d'Israël par mon ardeur.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
C'est pourquoi, dis-lui: Voici, je lui donne mon alliance de paix.
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
Et l'alliance de Sacrificature perpétuelle sera tant pour lui, que pour sa postérité après lui, parce qu'il a été animé de zèle pour son Dieu, et qu'il a fait propitiation pour les enfants d'Israël.
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
Et le nom de l'homme Israélite tué, lequel fut tué avec la Madianite, était Zimri, fils de Salu, chef d'une maison de père des Siméonites.
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
Et le nom de la femme Madianite qui fut tuée était Cozbi, fille de Tsur, chef du peuple, et de maison de père en Madian.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
Serrez de près les Madianites, et les frappez.
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
Car ils vous ont serrés [les premiers] par leurs ruses, par lesquelles ils vous ont surpris dans le fait de Péhor, et dans le fait de Cozbi, fille d'un des principaux d'entre les Madianites, leur sœur, qui a été tuée le jour de la plaie arrivée pour le fait de Péhor.

< Ƙidaya 25 >